Home Labarai ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 60 a jihar...

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 60 a jihar Kaduna

‘Yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa sun yi garkuwa da mutam 61 a kauyen Buda dake karamar hukumar Kajuru, a jihar Kaduna dake ARewa maso yammacin Nijeriya.

jaridar PUNCH ta ruwaito cewa ‘yan bindiga sun shiga garin ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar litinin inda suka yi garkuwa da mutane.

kawo yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar basu ce komai ba kan lamarin, sai dai mazauna kauyen sun bayyanawa jaridar yadda lamarin ya faru.

wani mazaunin kauyen Dauda Kajuru, yace masu garkuwar da mutane domin karbar kudin fansa sun yiwa garin tsinke inda suka fara harbin kan mai uwa da wabi.

“Akwai ‘yan uwa na cikin wadanda suka yi garkuwa da su a jiya, sai dai labarin da muke samu a safiyar nan da ‘yan bindiggar da wadanda aka yi garkuwa da su din sun isa inda suka nufa,” cewar Manyu.

yace tun bayna da aka cire kwamandan rundunar soji da aka fi sani da (Tega) ayyukan ‘yan bindiga ya cigaba da karuwa a kauyukan karamar hukumar Kajuru.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da raiKatu ta sami Nnamdi Kanu da laifukan ta'addanciSAEMA 2025: IMPR Ta kaddamar da Littafi Kan Yaki da Sha da fatauci miyagun ƙwayoyi da fasa kwauriSEAMA ta karrama Shugaban NDLEA, da wasu Manyan Jami'an tsaroNa kadu matuka da sace Dalibai 'yan mata a jihar Kebbi - TinubuKwankwaso ya nuna damuwarsa bisa sake dawowar rashin tsaro a NijeriyaMa'aikatan lantarki sun yi barazanar katse wuta a faɗin NajeriyaSERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake zargin sun yi ɓatan daboRundunar 'yan sanda Abuja ta Musanta yunkurin hallaka Lt. Ahmed YerimaBabu sauran sakaci a jam'iyyarmu ta PDP - Kabiru TurakiGwamnatin Najeriya ta dakatar da fara karɓar harajin man feturRikici tsakanin Boko Haram da ISWAP ya yi ajalin mayaƙa sama daLikitoci masu neman ƙwarewa na yajin aiki a NajeriyaNajeriya na maraba da taimakon Amurka idan za a kare martabarta'Trump ya nanata aniyarsa ta iya ƙaddamar da hari a Najeriya
X whatsapp