Home Labarai ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 60 a jihar...

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 60 a jihar Kaduna

‘Yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa sun yi garkuwa da mutam 61 a kauyen Buda dake karamar hukumar Kajuru, a jihar Kaduna dake ARewa maso yammacin Nijeriya.

jaridar PUNCH ta ruwaito cewa ‘yan bindiga sun shiga garin ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar litinin inda suka yi garkuwa da mutane.

kawo yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar basu ce komai ba kan lamarin, sai dai mazauna kauyen sun bayyanawa jaridar yadda lamarin ya faru.

wani mazaunin kauyen Dauda Kajuru, yace masu garkuwar da mutane domin karbar kudin fansa sun yiwa garin tsinke inda suka fara harbin kan mai uwa da wabi.

“Akwai ‘yan uwa na cikin wadanda suka yi garkuwa da su a jiya, sai dai labarin da muke samu a safiyar nan da ‘yan bindiggar da wadanda aka yi garkuwa da su din sun isa inda suka nufa,” cewar Manyu.

yace tun bayna da aka cire kwamandan rundunar soji da aka fi sani da (Tega) ayyukan ‘yan bindiga ya cigaba da karuwa a kauyukan karamar hukumar Kajuru.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kaiGwamnonin PDP na taro a ZamfaraYa kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai - MusaHukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kanokotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele KyariAna neman mutane 40 a cikin Kogi bayan kifewar kwale-kwale a SokotoA biya mu haƙƙoƙinmu, ba mu son bashin gwamnati - ASUUAmurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyiEFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsareMajalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din RanoƘananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasaAtiku Abubakar ya magantu kan tsare Tambuwal da EFCC ta yiPDP ta zargi APC da yunkurin kawo tasgaro a DamukradiyyaFadar Shugaban ƙasa ta musanta raɗe-raɗin rashin lafiyar Tinubu
X whatsapp