Home Labarai ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 60 a jihar...

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane sama da 60 a jihar Kaduna

‘Yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa sun yi garkuwa da mutam 61 a kauyen Buda dake karamar hukumar Kajuru, a jihar Kaduna dake ARewa maso yammacin Nijeriya.

jaridar PUNCH ta ruwaito cewa ‘yan bindiga sun shiga garin ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar litinin inda suka yi garkuwa da mutane.

kawo yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar basu ce komai ba kan lamarin, sai dai mazauna kauyen sun bayyanawa jaridar yadda lamarin ya faru.

wani mazaunin kauyen Dauda Kajuru, yace masu garkuwar da mutane domin karbar kudin fansa sun yiwa garin tsinke inda suka fara harbin kan mai uwa da wabi.

“Akwai ‘yan uwa na cikin wadanda suka yi garkuwa da su a jiya, sai dai labarin da muke samu a safiyar nan da ‘yan bindiggar da wadanda aka yi garkuwa da su din sun isa inda suka nufa,” cewar Manyu.

yace tun bayna da aka cire kwamandan rundunar soji da aka fi sani da (Tega) ayyukan ‘yan bindiga ya cigaba da karuwa a kauyukan karamar hukumar Kajuru.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan SiyasaJam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPPGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPPAmurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare KiristociShugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurkarahotannin daga jihar Katsina na cewa 'Yan bindiga sun kashe mutum 9 a jihar'Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026'Trump ya dakatar da bada biza ga ƴan Najeriya da wasu ƙasashe 74 ke fara aikiMayakan Boko Haram sun kutsa cikin ayarin sojin Najariya da bama-bamai a BornoSojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin TimbuktuAbba da Tinubu sun tattauna kan tsaro da ci gaban Kano - Dawakin TofaƳanbindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 160 a coci a KadunaMun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano - NHRCƳansanda a jihar Nasarawa sun tseratar da yara 17 da ake shirin safararsuSojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya
X whatsapp