Home Labarai ‘Yan bindiga sun sace mata masu Juna biyu a jihar Katsina

‘Yan bindiga sun sace mata masu Juna biyu a jihar Katsina

Wani harin ‘Yan bindiga a garin Na-Alma dake  yankin karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina, yayi sanadiyyar batan mutane masu tarin yawa galibi mata har da masu juna biyu, da kananan yara, tare da kona gidaje,  da wani wanda ‘yan bindiga suka taba sare wa hannu da kafa, bayan kashe wani mai unguwa.

Rahotannin sun bayanai cewa, hare-haren ‘yan bindigan na baya-bayan nan sun jefa mutane da dama cikin tasku.

Wani mutumin yankin, wanda ya tsallake rijiya da baya ya ce suna cikin rudani, kuma kashi takwas cikin goma na mutanen garin sun yi kaura.

Mutumin ya kuma ce sun shaida wa jami’an tsaro cewa sun samu bayanan sirri na harin da ‘yan bindigar za su kai garin nasu.

“Tun wajen takwas da rabi na dare muka shaida wa jami’an tsaro amman ba su zo ba har sai da mutanen nan suka shiga suka fara harbi, sai dai kawai su ce ga su nan zuwa, amman ba su zo ba har sai da ‘yan bindiga suka gama kone-kone da duk abin da za su yi sannan suka zo.”

Jihar Katsina dai na guda cikin jihohin Arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro, duk da cewa mahukunta a jihar na bugun kirjin cewa sun daukar matakan da suka dace domin magance matsalar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp