Home Labarai ‘Yan bindiga sun sace mata masu Juna biyu a jihar Katsina

‘Yan bindiga sun sace mata masu Juna biyu a jihar Katsina

Wani harin ‘Yan bindiga a garin Na-Alma dake  yankin karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina, yayi sanadiyyar batan mutane masu tarin yawa galibi mata har da masu juna biyu, da kananan yara, tare da kona gidaje,  da wani wanda ‘yan bindiga suka taba sare wa hannu da kafa, bayan kashe wani mai unguwa.

Rahotannin sun bayanai cewa, hare-haren ‘yan bindigan na baya-bayan nan sun jefa mutane da dama cikin tasku.

Wani mutumin yankin, wanda ya tsallake rijiya da baya ya ce suna cikin rudani, kuma kashi takwas cikin goma na mutanen garin sun yi kaura.

Mutumin ya kuma ce sun shaida wa jami’an tsaro cewa sun samu bayanan sirri na harin da ‘yan bindigar za su kai garin nasu.

“Tun wajen takwas da rabi na dare muka shaida wa jami’an tsaro amman ba su zo ba har sai da mutanen nan suka shiga suka fara harbi, sai dai kawai su ce ga su nan zuwa, amman ba su zo ba har sai da ‘yan bindiga suka gama kone-kone da duk abin da za su yi sannan suka zo.”

Jihar Katsina dai na guda cikin jihohin Arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro, duk da cewa mahukunta a jihar na bugun kirjin cewa sun daukar matakan da suka dace domin magance matsalar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp