Gwamna Kano ya rantsar da sabbin kwamishinoni a jihar

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rantsar da sabbin kwamishinoni guda hudu tare da bayyana ma’aikatan da za su fara aiki.

Gwamna Yusuf ya jagoranci rantsar da sabbin Kwamishinonin ne a dakin taro na Africa House dake gidan gwamnatin jihar kano.

Gwamnan ya bayyana Mustapha Rabi’u kwankwaso a matsayin kwamishinan ma’aikatar matasa da wasanni, sai Abduljabbar Garko a matsayin kwamishinan kasa da safayo na jihar kano, yayin da aka tura Shehu Aliyu yarmedi a matsayin kwamishinan aiyuka na musamman sai Adamu Aliyu kibiya kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar.

Gwamna Yusuf ya Kuma ja hankalinsu da su zama masu gaskiya da rikon Amana a dukkannin al’muransu na yau da kullum.

Ya kuma bukace su da su maida hankali wajen bashi damar sauke nauyin da al’ummar jihar kano suka dora masa.

Idan za’a iya tunawa majalisar dokokin jihar kano tun a watan da ya gabata ne ta kammala aikin tantance sunayen sabbin Kwamishinonin da gwamnan ya tura mata  domin nada su a matsayin Kwamishinoni.

Duk dai a wannan rana gwamnan ya jagoranci rantsar da sabbin masu bashi shawara da suma majalisar dokokin jihar kano ta sahalle masa ya nada su.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 18 hours 1 minute 47 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 43 minutes 12 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com