Home Labarai Farashin Iskar Gas (LPG) ya sauko a Nigeria

Farashin Iskar Gas (LPG) ya sauko a Nigeria

 

Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa farashin gas din girki (LPG) ya fara sauka a kasar sakamakon faduwar darajar dala da habakar darajar Naira a kasuwar kasar.

Idan dai za a iya tunawa a ‘yan tskanin nan AL’ummar Nijeriya suka koka kan yadda farashin Iskar gas din tayi tashi gwauron zabi, abin da suka bukaci mahukunta a kasar da su sanya baki domin ganin an sami sauki.

Ko dai a watan Maris din daya gabata an sayar da gas din na girki a kan farashin Naira 1,500 ko wannen (kg), sai dai sakamakon faduwar dalar a kasuwar chanjin Nijeriya yasa yanzu haka ake sayar da iskar gas din kan farashin Naira 1,100.

Jaridar Economic confidential ta rawaito cewa a wajen sayar da iskar Gas na Iju-ishaga dake jihar Legas ana sayar da iskar gas din naira 1,100 dukkan (kg) an sami ragi kan yadda aka sayar a watan Maris din daya gabata.

Ana dai sa ran farashin zai cigaba da sauka idan babban bankin kasar ya cigaba da kokarin da yake na farfado da darajar Naira a kasuwar chanji ta duniya, tare da sanya idanu kan ‘yan kasuwa wadan ake zargi da tsawwala AL’ummar kasar.

PRNigeria Hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp