Home Labarai An janye ‘yan sandan dake gadin Yahaya Bello

An janye ‘yan sandan dake gadin Yahaya Bello

Babban Sufeto ‘yan sandan Najeriya IGP Olukayode Egbetokun, ya bayar da umarnin janye dukkan jami’an ‘yan sandan da ke gadin tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.

Wannan na kunshe ta cikin wata takar da mai dauke da adireshin hedkwatar ‘yan sandan Najeriya da aka aika zuwa MOPL 37 a Lokoja.

Takardar mai lamba: “CB:4001/DOPS/PMF/FHQ/ABJ/VOL.48/34 ta bayyana cewa, “babban Sefeton ‘yan sandan Nijeriya ya ba da umarnin janye dukkan ‘yan sandan da ke raka tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis din da ta gabata ne Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a wata takarda da ta fitar ta sanya tsohon Gwamnan cikin jerin sunayen wadanda zasu fara farauta.

Wannan dai ya biyo bayan rashin nasarar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta yi na kama Yahaya Bello a gidansa da ke Abuja, sakamakon zarginsa da ake da karkatar da kudade har N80.2billion.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp