Home Labarai An janye ‘yan sandan dake gadin Yahaya Bello

An janye ‘yan sandan dake gadin Yahaya Bello

Babban Sufeto ‘yan sandan Najeriya IGP Olukayode Egbetokun, ya bayar da umarnin janye dukkan jami’an ‘yan sandan da ke gadin tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.

Wannan na kunshe ta cikin wata takar da mai dauke da adireshin hedkwatar ‘yan sandan Najeriya da aka aika zuwa MOPL 37 a Lokoja.

Takardar mai lamba: “CB:4001/DOPS/PMF/FHQ/ABJ/VOL.48/34 ta bayyana cewa, “babban Sefeton ‘yan sandan Nijeriya ya ba da umarnin janye dukkan ‘yan sandan da ke raka tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis din da ta gabata ne Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a wata takarda da ta fitar ta sanya tsohon Gwamnan cikin jerin sunayen wadanda zasu fara farauta.

Wannan dai ya biyo bayan rashin nasarar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta yi na kama Yahaya Bello a gidansa da ke Abuja, sakamakon zarginsa da ake da karkatar da kudade har N80.2billion.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp