Home Labarai ‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

Tun bayan da gwamnatin Nijeriya ta haramta biyan kudin fansa, tare da barin wuta da sojojin kasar ke yi kan ‘yan bindigar daji, guda cikin shuwagabannin kungiyoyin ‘yan ta’addan dajin masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa ya nemi sulhu.

Wannan dai na zuwa ne tun bayan da mai bawa shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa gwamantin tarayya ta haramta biyan kudin fansa domin kubutar da wadanda da masu garkuwa da mutane suka kama.

Shugaban ‘yan ta’addan da ya kira kansa Gabar Haliyu, da yake Magana da turancin Pigin inda yake jawabi ga mambobin dabar sa.

Ta cikin wani faifan bidiyo da PRNigeria ta samu, haliyu na bayyana cewa biyan fansar wajibi ne domin tseratar da rayuka, da kuma barin Gwamnan jihar zamfara Dauda Lawan Dare ya gudanar da mulki cikin kwanciyar hankali.

Haka dai PRNigeria ta tattara cewa manyan masu fada a ji a cikin Fulani da aka fi sani da Ardo sun bukaci ‘yan ta’addan da su aje makamansu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp