Home Labarai ‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

Tun bayan da gwamnatin Nijeriya ta haramta biyan kudin fansa, tare da barin wuta da sojojin kasar ke yi kan ‘yan bindigar daji, guda cikin shuwagabannin kungiyoyin ‘yan ta’addan dajin masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa ya nemi sulhu.

Wannan dai na zuwa ne tun bayan da mai bawa shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa gwamantin tarayya ta haramta biyan kudin fansa domin kubutar da wadanda da masu garkuwa da mutane suka kama.

Shugaban ‘yan ta’addan da ya kira kansa Gabar Haliyu, da yake Magana da turancin Pigin inda yake jawabi ga mambobin dabar sa.

Ta cikin wani faifan bidiyo da PRNigeria ta samu, haliyu na bayyana cewa biyan fansar wajibi ne domin tseratar da rayuka, da kuma barin Gwamnan jihar zamfara Dauda Lawan Dare ya gudanar da mulki cikin kwanciyar hankali.

Haka dai PRNigeria ta tattara cewa manyan masu fada a ji a cikin Fulani da aka fi sani da Ardo sun bukaci ‘yan ta’addan da su aje makamansu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp