Home Labarai ‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

Tun bayan da gwamnatin Nijeriya ta haramta biyan kudin fansa, tare da barin wuta da sojojin kasar ke yi kan ‘yan bindigar daji, guda cikin shuwagabannin kungiyoyin ‘yan ta’addan dajin masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa ya nemi sulhu.

Wannan dai na zuwa ne tun bayan da mai bawa shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa gwamantin tarayya ta haramta biyan kudin fansa domin kubutar da wadanda da masu garkuwa da mutane suka kama.

Shugaban ‘yan ta’addan da ya kira kansa Gabar Haliyu, da yake Magana da turancin Pigin inda yake jawabi ga mambobin dabar sa.

Ta cikin wani faifan bidiyo da PRNigeria ta samu, haliyu na bayyana cewa biyan fansar wajibi ne domin tseratar da rayuka, da kuma barin Gwamnan jihar zamfara Dauda Lawan Dare ya gudanar da mulki cikin kwanciyar hankali.

Haka dai PRNigeria ta tattara cewa manyan masu fada a ji a cikin Fulani da aka fi sani da Ardo sun bukaci ‘yan ta’addan da su aje makamansu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp