Home DUNIYA Ana cigaba da Jimami a kasar Kenya bayan mutuwa babban Hafsan sojin...

Ana cigaba da Jimami a kasar Kenya bayan mutuwa babban Hafsan sojin kasar

Ana cigaba da zaman makoki na kwanaki uku a ƙasar Kenya don jimamin mutuwar babban hafsan hafsoshin tsaron kasar (CDF) Janar Francis Omondi Ogolla wanda ya mutu a wani jirgin sama da ya yi hatsari a lardin Elgeyo Marakwet da ke arewa maso yammacin kasar.

Ogolla, mai shekaru 61, ya mutu ne ranar Alhamis tare da wasu jami’an soji 9 da suka yi masa rakiya zuwa wani aiki na tantance yanayin tsaro a yankunan arewa maso yammacin Kenya da ke fama da matsalar rashin tsaro.

A wani jawabi da ya yi wa al’ummar kasar sa’o’i bayan hatsarin jirgin, shugaba William Ruto ya ce Kenya ta yi asarar “ɗaya daga cikin manyan hafsoshinta”.

Tsohon shugaban ƙasar Uhuru Kenyatta da jagoran ‘yan adawa Raila Odinga da jakadiyar Amurka Meg Whitman na daga cikin jagororin da suka yi ta’aziyyar mutuwar babban jami’in sojin na Kenya.

Marigayi Janar ɗin ya shiga rundunar sojojin Kenya (KDF) a shekara ta 1984 kuma ya kai matsayin babban kwamandan sojojin ƙasar a bara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp