Home DUNIYA Ana cigaba da Jimami a kasar Kenya bayan mutuwa babban Hafsan sojin...

Ana cigaba da Jimami a kasar Kenya bayan mutuwa babban Hafsan sojin kasar

Ana cigaba da zaman makoki na kwanaki uku a ƙasar Kenya don jimamin mutuwar babban hafsan hafsoshin tsaron kasar (CDF) Janar Francis Omondi Ogolla wanda ya mutu a wani jirgin sama da ya yi hatsari a lardin Elgeyo Marakwet da ke arewa maso yammacin kasar.

Ogolla, mai shekaru 61, ya mutu ne ranar Alhamis tare da wasu jami’an soji 9 da suka yi masa rakiya zuwa wani aiki na tantance yanayin tsaro a yankunan arewa maso yammacin Kenya da ke fama da matsalar rashin tsaro.

A wani jawabi da ya yi wa al’ummar kasar sa’o’i bayan hatsarin jirgin, shugaba William Ruto ya ce Kenya ta yi asarar “ɗaya daga cikin manyan hafsoshinta”.

Tsohon shugaban ƙasar Uhuru Kenyatta da jagoran ‘yan adawa Raila Odinga da jakadiyar Amurka Meg Whitman na daga cikin jagororin da suka yi ta’aziyyar mutuwar babban jami’in sojin na Kenya.

Marigayi Janar ɗin ya shiga rundunar sojojin Kenya (KDF) a shekara ta 1984 kuma ya kai matsayin babban kwamandan sojojin ƙasar a bara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp