Home Labarai Ruftawar kasa ta hallaka yara takwas a jihar Kebbi

Ruftawar kasa ta hallaka yara takwas a jihar Kebbi

Kimanin yara takwas sun mutun bayan ƙasar gini ta rufta musu a mahaƙar ƙasar ginin ta Dustin Dukku da ke unguwar Badariya a ƙaramar hukumar Birnin Kebbi a jihar Kebbi.

Shugaban ƙaramar hukumar Hon. Muhammad Dahiru Ambursa, ya tabbatar wa da sashen hausa na BBC faruwar lamarin, inda ya ce tuni aka fara shirye-shiryen yi wa yaran jana’iza.

Ya kuma ce akwai wasu ƙarin yara biyu da suka jikkata ciki har da wanda ya karye a ƙafa.

To sai dai wani mutum da abin ya faru a gaban idonsa ya shaida cewa yara tara ne suka rasu, lokacin iftila’in da ya faru da safiyar ranar Asabar

Shugaban karamar hukumar ya ce mafi yawa daga cikin yaran da lamarin ya rutsa da su almajirai ne waɗanda ke aikin haƙar ƙasar gini a yankin.

Honarabul Ambursa ya ce ya bayar da umarnin dakatar da haƙar ƙasar gini a wurin.

”Mun bayar da umarnin killace wurin da waya tare da saka alamar da ke nuna cewa an hana haƙar ƙasar gini a wurin, mun kuma buƙaci hakimai da sauran iyayen ƙasa da su saka a yi shela, don hana mutane haƙar ƙasar gini a wannan wuri”, in ji shi.

Masu ƙaramin ƙarfi dai kan yi amfani da ƙasa wajen yin bulon ƙasa da za su yi amfani da shi wajen yin gine-ginen musamman a garuruwa da ƙauyuka a Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp