Home Labarai Farashin Iskar Gas (LPG) ya sauko a Nigeria

Farashin Iskar Gas (LPG) ya sauko a Nigeria

 

Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa farashin gas din girki (LPG) ya fara sauka a kasar sakamakon faduwar darajar dala da habakar darajar Naira a kasuwar kasar.

Idan dai za a iya tunawa a ‘yan tskanin nan AL’ummar Nijeriya suka koka kan yadda farashin Iskar gas din tayi tashi gwauron zabi, abin da suka bukaci mahukunta a kasar da su sanya baki domin ganin an sami sauki.

Ko dai a watan Maris din daya gabata an sayar da gas din na girki a kan farashin Naira 1,500 ko wannen (kg), sai dai sakamakon faduwar dalar a kasuwar chanjin Nijeriya yasa yanzu haka ake sayar da iskar gas din kan farashin Naira 1,100.

Jaridar Economic confidential ta rawaito cewa a wajen sayar da iskar Gas na Iju-ishaga dake jihar Legas ana sayar da iskar gas din naira 1,100 dukkan (kg) an sami ragi kan yadda aka sayar a watan Maris din daya gabata.

Ana dai sa ran farashin zai cigaba da sauka idan babban bankin kasar ya cigaba da kokarin da yake na farfado da darajar Naira a kasuwar chanji ta duniya, tare da sanya idanu kan ‘yan kasuwa wadan ake zargi da tsawwala AL’ummar kasar.

PRNigeria Hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp