Home Labarai ‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

‘Yan bindiga sun fara neman sulhu a Nijeriya

Tun bayan da gwamnatin Nijeriya ta haramta biyan kudin fansa, tare da barin wuta da sojojin kasar ke yi kan ‘yan bindigar daji, guda cikin shuwagabannin kungiyoyin ‘yan ta’addan dajin masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa ya nemi sulhu.

Wannan dai na zuwa ne tun bayan da mai bawa shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa gwamantin tarayya ta haramta biyan kudin fansa domin kubutar da wadanda da masu garkuwa da mutane suka kama.

Shugaban ‘yan ta’addan da ya kira kansa Gabar Haliyu, da yake Magana da turancin Pigin inda yake jawabi ga mambobin dabar sa.

Ta cikin wani faifan bidiyo da PRNigeria ta samu, haliyu na bayyana cewa biyan fansar wajibi ne domin tseratar da rayuka, da kuma barin Gwamnan jihar zamfara Dauda Lawan Dare ya gudanar da mulki cikin kwanciyar hankali.

Haka dai PRNigeria ta tattara cewa manyan masu fada a ji a cikin Fulani da aka fi sani da Ardo sun bukaci ‘yan ta’addan da su aje makamansu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp