Home Labarai EFCC ta kama ‘yan damfara 28 a birnin Abuja

EFCC ta kama ‘yan damfara 28 a birnin Abuja

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta sami nasarara kama mutane 28 da ake zargi da Damfara a birnin tarayya Nijeriya Abuja.

Wannan ya biyo bayan wani simame da dakarun hukumar dake shiyyar birnin tarayya suka gudanar kan wadanda ake zargin da ayyukan damfarar ta yanar gizo.

Ta cikin wata sanarwa da sashin yada labarai da hulda da jama’a na hukumar ya fitar, yace an sami nasarar kama mutanen ne a yankin Gwarimpa da Katampe dake birnin bayan samun bayanai kan yadda suke gudanar da ayyukan na damfara.

Sanarwar ta kara da cewa dakarun sun sami wayoyin hannun guda 43 kirar kamfanoni da dama sai kuma abin hawa da kuma agoggunan zamani (Smart watches) a hannun wadanda ake zargin.

Daga bisani  hukumar ta tabbatar da shirin ta na gurfanar da su gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp