Home Labarai Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan Bindiga a Adamawa

Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan Bindiga a Adamawa

Dakarun sojojin Najeriya da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabashin kasar tare da rundunar haɗin gwiwar sojoji da ƴan sa-kai sun yi nasarar kame wasu gungun ‘yan ta’adda da ke kan hanyarsu ta kai hari a karamar hukumar Yola ta Kudu a jihar Adamawa.

ta cikin wata wallafa da Rundunar sojin Najeriyar ta yi a shafinta na X, ta ce dakarunta sun ci karo da ƴan ta’addar da ke shirin kai wa al’ummar hari ne a lokacin da suke sintiri a kusa da Wuro Jabbe.

Ta kuma ce anyi zazzafar musayar wuta tsakanin sojojin da ƴan ta’adda abin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan mika wuya tare da barin makamansu. Sojojin sun kuma ƙwace makamai da harsasai 402.

A wani samame na daban kuma amma mai alaka da wannan, sojojin sun ce sun kama wasu mutane uku da ake zargi da harbin bindiga a yankin Sukuk, da ke karamar hukumar Madagali ta jihar. An kama waɗanda ake zargin da makamai da dama.

Sojojin Najeriya na ci gaba da taka-tsan-tsan tare da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankunan ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp