Home Labarai Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan Bindiga a Adamawa

Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan Bindiga a Adamawa

Dakarun sojojin Najeriya da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabashin kasar tare da rundunar haɗin gwiwar sojoji da ƴan sa-kai sun yi nasarar kame wasu gungun ‘yan ta’adda da ke kan hanyarsu ta kai hari a karamar hukumar Yola ta Kudu a jihar Adamawa.

ta cikin wata wallafa da Rundunar sojin Najeriyar ta yi a shafinta na X, ta ce dakarunta sun ci karo da ƴan ta’addar da ke shirin kai wa al’ummar hari ne a lokacin da suke sintiri a kusa da Wuro Jabbe.

Ta kuma ce anyi zazzafar musayar wuta tsakanin sojojin da ƴan ta’adda abin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan mika wuya tare da barin makamansu. Sojojin sun kuma ƙwace makamai da harsasai 402.

A wani samame na daban kuma amma mai alaka da wannan, sojojin sun ce sun kama wasu mutane uku da ake zargi da harbin bindiga a yankin Sukuk, da ke karamar hukumar Madagali ta jihar. An kama waɗanda ake zargin da makamai da dama.

Sojojin Najeriya na ci gaba da taka-tsan-tsan tare da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankunan ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp