Home Labarai EFCC ta kama ‘yan damfara 28 a birnin Abuja

EFCC ta kama ‘yan damfara 28 a birnin Abuja

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta sami nasarara kama mutane 28 da ake zargi da Damfara a birnin tarayya Nijeriya Abuja.

Wannan ya biyo bayan wani simame da dakarun hukumar dake shiyyar birnin tarayya suka gudanar kan wadanda ake zargin da ayyukan damfarar ta yanar gizo.

Ta cikin wata sanarwa da sashin yada labarai da hulda da jama’a na hukumar ya fitar, yace an sami nasarar kama mutanen ne a yankin Gwarimpa da Katampe dake birnin bayan samun bayanai kan yadda suke gudanar da ayyukan na damfara.

Sanarwar ta kara da cewa dakarun sun sami wayoyin hannun guda 43 kirar kamfanoni da dama sai kuma abin hawa da kuma agoggunan zamani (Smart watches) a hannun wadanda ake zargin.

Daga bisani  hukumar ta tabbatar da shirin ta na gurfanar da su gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp