Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan Bindiga a Adamawa

Dakarun sojojin Najeriya da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabashin kasar tare da rundunar haɗin gwiwar sojoji da ƴan sa-kai sun yi nasarar kame wasu gungun ‘yan ta’adda da ke kan hanyarsu ta kai hari a karamar hukumar Yola ta Kudu a jihar Adamawa.

ta cikin wata wallafa da Rundunar sojin Najeriyar ta yi a shafinta na X, ta ce dakarunta sun ci karo da ƴan ta’addar da ke shirin kai wa al’ummar hari ne a lokacin da suke sintiri a kusa da Wuro Jabbe.

Ta kuma ce anyi zazzafar musayar wuta tsakanin sojojin da ƴan ta’adda abin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan mika wuya tare da barin makamansu. Sojojin sun kuma ƙwace makamai da harsasai 402.

A wani samame na daban kuma amma mai alaka da wannan, sojojin sun ce sun kama wasu mutane uku da ake zargi da harbin bindiga a yankin Sukuk, da ke karamar hukumar Madagali ta jihar. An kama waɗanda ake zargin da makamai da dama.

Sojojin Najeriya na ci gaba da taka-tsan-tsan tare da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankunan ƙasar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 8 minutes 28 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 49 minutes 53 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com