ISWAP ta Gargadi mazauna Kauyen Kukawa dake jihar Borno

Mayaƙan ISWAP sun bai wa mazauna kauyen Kukawa lga sanarwar su bar kauyensu ko kuma su fuskanci kisa, kwanaki huɗu da hallaka masunta goma sha biyar a yankin Tumbun Rogo.

tunu wasu cikin mazauna kauyen suka fara guduwa sa’oi kadan bayan da suka sami wannan sanarwa kamar yadda jaridar Emergency Digest ta ruwaito.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaye sunansa, ya bayyana cewa mayakan sun tara jama’ar al’umma daban-daban a ƙaramar hukumar da sanyin safiyar Alhamis, inda suka ce su bar gidajensu kafin ranar Asabar, in ba haka ba za a kashe su.

A cewarsa, bayan da suka samu barazanar ‘yan ISWAP din, al’ummomin suka fara barin yankunansu, yayin da wasu suka tafi Kross Kauwa, wasu kuma suka tafi Monguno.

Kukawa lga ƙaramar hukuma ce a gefen tafkin Chadi wadda ta shahara wajen kamun kifi da noma, kuma akwai dakarun sojojin Najeriya da na ruwa.

Duk da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, mayaƙan Boko Haram/ISWAP na ci gaba da kai hare-hare a cikin al’ummomin

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 9 hours 41 minutes 58 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 11 hours 23 minutes 23 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com