Home General Ma’aikatan Nijeriya zasu rabauta da horon Tattara bayanai

Ma’aikatan Nijeriya zasu rabauta da horon Tattara bayanai

Gwamnatin tarayyar kasar Nijeriya ta kaddamar da wani shiri na horas da ma’aikatanta dubu 10 hanyoyin tattara bayanai na zamani domin gudanar da ayyukan su cikin tsari.

Hukumar dake lura da bayanai ta kasar nan wato Nigeria Data Protection Commission da hadin gwiwar Data.org ne suka shirya gudanar da shirin, domin horas da ma’aikatan gwamnatin tarayyar kasar nan abinda dokar tattara bayyanai ta shekarar 2023 ta kunsa domin sanya su a turbar data dace wajen gudanar da ayyukan su.

Ministan yada labarai, kirkire-kirkire da tattalin arziki na zamani, Dr. Bosun Tijjani yace hadin gwiwa tsakanin hukumar ta NDPC da Data.org kamar wani somin tabi ne cikin a yunkurin hukumar na daidaita ayyukan ma’aikatan Gwamnatin tarayya tare da inganta musu shi da ilimi da dabaru.

Wadanda zasu rabauta da wannan horo dai sun hadar da shuwagabanin bayanai, manyan dakarun tattara bayanan tsaro, da kuma da kuma masu lura da tattara bayanai gami da masu kula da tsaron na’ura mai kwakwalwa wanda ke aiki a ma’aikatun gwamnatin tarayya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp