Home General Ma’aikatan Nijeriya zasu rabauta da horon Tattara bayanai

Ma’aikatan Nijeriya zasu rabauta da horon Tattara bayanai

Gwamnatin tarayyar kasar Nijeriya ta kaddamar da wani shiri na horas da ma’aikatanta dubu 10 hanyoyin tattara bayanai na zamani domin gudanar da ayyukan su cikin tsari.

Hukumar dake lura da bayanai ta kasar nan wato Nigeria Data Protection Commission da hadin gwiwar Data.org ne suka shirya gudanar da shirin, domin horas da ma’aikatan gwamnatin tarayyar kasar nan abinda dokar tattara bayyanai ta shekarar 2023 ta kunsa domin sanya su a turbar data dace wajen gudanar da ayyukan su.

Ministan yada labarai, kirkire-kirkire da tattalin arziki na zamani, Dr. Bosun Tijjani yace hadin gwiwa tsakanin hukumar ta NDPC da Data.org kamar wani somin tabi ne cikin a yunkurin hukumar na daidaita ayyukan ma’aikatan Gwamnatin tarayya tare da inganta musu shi da ilimi da dabaru.

Wadanda zasu rabauta da wannan horo dai sun hadar da shuwagabanin bayanai, manyan dakarun tattara bayanan tsaro, da kuma da kuma masu lura da tattara bayanai gami da masu kula da tsaron na’ura mai kwakwalwa wanda ke aiki a ma’aikatun gwamnatin tarayya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp