Majalisar Dattijai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta cigaba da biyan ma’aikta tsohon Albashi

Majalisar Dattijan Nijeriya ta bukaci Gwamnatin tarayyar kasar data ci gaba da biyan naira dubu 35 matsayin mafi karancin albashi a kasar, kasancewar ba’a cimma matsaya kan Karin mafi karancin Albashin.

Shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio ne ya bayyana hakan a karshen ganawar sa’oi 4 tsakanin kungiyoyin kwadagon da wakilan gwamnatin tarayya bisa shirin kungiyoyin na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

Akpabio ya kuma roki kungiyoyin na kwadago da su jenye yajin aikin saboda ‘yan Nijeriya da ci gaban kasar.

Sai dai ministan yada labarai da wayar da kai Alhaji Muhammad Idris, yace matsayar gwamnatin shine zata cigaba da biyan tsohon albashin har sai tattaunar ta kammala.

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 36 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 18 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com