Home General Kungiyoyin a Nijeriya Kwadago sun fara yajin aiki a ranar litinin

Kungiyoyin a Nijeriya Kwadago sun fara yajin aiki a ranar litinin

An wayi gari da yakin aikin kungiyoyin kwadago a Nijeriya abin da ake tsammanin Akwai yiyuwar ayyukan tattalin arziki a kasar su tsaya cik sanadin yajin aikin.

Kokarin da shuwagabannin Majalisar dokokin kasar suka yi domin sasanta bangarorin ya ci-tura.

Bayan ganawar sa’o’i hudu da shugabannin Majalisar dokokin kasar da yammacin ranar Lahadi a Abuja, shugabannin kungiyar kwadagon sun ce babu gudu babu ja da baya game da yajin aikin gama gari da aka shirya ya fara ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Sai dai shugaban kungiyar kwadago ta TUC, Festus Osifo ya ce za su tunbi sauran reshoshinsu a kan kiran da shugabannin Majalisar suka yi mu su ma a kan su janye yajin aikin.

“A yanzu ba mu da hurumin janye yajin aikin, yajin aikin zai fara ne yayin da mu mika rokon da shugabbanin Majalisar dokokin kasar suka yi ga rassan mu daban-daban, game da kiran da suka yi a kan mu janye yajin aikin” inji shi.

Tun da farko, Osifo, shugaban kungiyar kwadago (TUC); da takwaransa na kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero; sun gana da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas. a Abuja.

Kungiyoyin kwadagon sun kira yajin aikin ne sakamakon rashin cimma matsaya a tattaunwar da bangarorin biyu ke yi da gwamnatin kasar kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata.

Kungiyoyin kwadago fiye da 10 sun yi kira ga ma’aikatansu da su amsa kiran uwar kungiyar kwadago ta kasa har sai abinda hali ya yi.

Ma’aikatan lafiya da bankunan kasuwanci da na sufurin jiragen sama da na sauran fanonin na cikin wadanda za su shiga yajin aiki, abinda ake ganin zai kawo nakasu ga tattalin arzikin kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp