Home General Kungiyoyin a Nijeriya Kwadago sun fara yajin aiki a ranar litinin

Kungiyoyin a Nijeriya Kwadago sun fara yajin aiki a ranar litinin

An wayi gari da yakin aikin kungiyoyin kwadago a Nijeriya abin da ake tsammanin Akwai yiyuwar ayyukan tattalin arziki a kasar su tsaya cik sanadin yajin aikin.

Kokarin da shuwagabannin Majalisar dokokin kasar suka yi domin sasanta bangarorin ya ci-tura.

Bayan ganawar sa’o’i hudu da shugabannin Majalisar dokokin kasar da yammacin ranar Lahadi a Abuja, shugabannin kungiyar kwadagon sun ce babu gudu babu ja da baya game da yajin aikin gama gari da aka shirya ya fara ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Sai dai shugaban kungiyar kwadago ta TUC, Festus Osifo ya ce za su tunbi sauran reshoshinsu a kan kiran da shugabannin Majalisar suka yi mu su ma a kan su janye yajin aikin.

“A yanzu ba mu da hurumin janye yajin aikin, yajin aikin zai fara ne yayin da mu mika rokon da shugabbanin Majalisar dokokin kasar suka yi ga rassan mu daban-daban, game da kiran da suka yi a kan mu janye yajin aikin” inji shi.

Tun da farko, Osifo, shugaban kungiyar kwadago (TUC); da takwaransa na kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero; sun gana da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas. a Abuja.

Kungiyoyin kwadagon sun kira yajin aikin ne sakamakon rashin cimma matsaya a tattaunwar da bangarorin biyu ke yi da gwamnatin kasar kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata.

Kungiyoyin kwadago fiye da 10 sun yi kira ga ma’aikatansu da su amsa kiran uwar kungiyar kwadago ta kasa har sai abinda hali ya yi.

Ma’aikatan lafiya da bankunan kasuwanci da na sufurin jiragen sama da na sauran fanonin na cikin wadanda za su shiga yajin aiki, abinda ake ganin zai kawo nakasu ga tattalin arzikin kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp