Home General Kotu ta bayar da belin Abba Kyari

Kotu ta bayar da belin Abba Kyari

Rahotannin na bayyana cewa kotu ta bayar da belin dakataccen mataimakain kwamishinan ‘yan sanda shugaban rundunar kai daukin gaggawa Abba Kyari, bayan zaman gidan gyaran hali na watanni 27.

Wannan na zuwa ne bayan hukuncin babbar kotun tarayya dake zamanta a birnin tarayya Abuja na bashi belin makwanni biyu.

Kotun ta ce an bayar da belin Abba kyari ne domin ya je gida ya kammala jana’idar Mahaifiyar.

Kotun data zauna ranar juma’a 31 ga watan mayun daya gabata, domin duba bukatar bayar da belin Kyari dake fuskantar tuhume-tuhume na ta’ammali da miyagun kwayoyi, biyo bayan kama shi da akayi a watan fabrerun shekarar 2022.

Kakakin hukumar kula da gidan gyaran hali da tarbiyya na birnin tarayya Abuja Admu Duza yace an bayar da belin kyari ne bayan ya cika wasu sharudda.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp