Rundunar ‘yan sanda Kano tayi holen bata gari 149 a jihar

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce ta kama mutum 149 da take zarginsu da ayyukan fashi da makami da daba da garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka cikin kwanaki 10 da suka gabata a jihar.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna ne ya bayyana haka a yayin da rundunar ‘yan sandan ke holen wadanda ake zargin gaban manema labarai bisa kamen da rundunar ta yi.

Ya ce an kama ƴan daba 106 da waɗanda ake zargi masu fashi da makami ne su 25 da mutum biyu da ake zargi suna garkuwa da mutane sai masu satar mota uku da dillalan miyagun ƙwayoyi uku a sassa daban-daban na jihar.

“Mun kuma gano motoci biyu da babura takwas da wuƙaƙe 58 da bindiga ɗaya da ƙunshi 87 na abin da ake zargin tabar wiwi ne.

Kiyawa ya ce kamen ya biyo bayan shawagin da ƴan sanda suke yi a sassan jihar domin hana aikata laifuka.

A cewarsa, mutanen da aka kama na sashen binciken manyan laifuka na rundunar inda ake gudanar da bincike a kan su.

Kwamishinan ƴan sanda na jihar, Salman Dogo Garba ya ce rundunar za ta ci gaba da aiki ba dare ba rana domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 22 minutes 52 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 4 minutes 17 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com