Home General Ricikin Manoma da makiyaya ya yi sanadin mutuwar mutum 2 a jihar...

Ricikin Manoma da makiyaya ya yi sanadin mutuwar mutum 2 a jihar Jigawa

Rundunar ‘yan sandan jihar jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum 2 tare da kone gidaje 3 bisa wata arangama tsakanin manoma da makiyaya a karamar hukumar Birnin Kudu dake jihar.

kakaikin rundunar ‘yan sandna jihar DSP Lawan Shiisu Adam ne ya tabbatar da hakan inda yace jami’an ‘yan sandan hadin gwiwa da jami’an tsaron Civil defence da kuma dakarun sa kai na bijilanti. sun sami nasarar kwantar da rikicin tare da kama mutum 5 da kuma shanu guda biyar da aka yasar.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa makiyayan da suka fito daga jihar Katsina, sun tasamma yankin da tarin garken shanu, inda suka fara lalata amfanin gonar da manoma suka shuka, wannan ne ya sanya manoman daukar matakin kare gonakinsu da rayukansu.

yace arangamar ta haddasa mutuwar mutum 2 daga ko wanne bangare tare da kone gidaje 3 mallakin alúmmar garin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp