Home DUNIYA Rundunar ‘yan sanda Kano tayi holen bata gari 149 a jihar

Rundunar ‘yan sanda Kano tayi holen bata gari 149 a jihar

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce ta kama mutum 149 da take zarginsu da ayyukan fashi da makami da daba da garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka cikin kwanaki 10 da suka gabata a jihar.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna ne ya bayyana haka a yayin da rundunar ‘yan sandan ke holen wadanda ake zargin gaban manema labarai bisa kamen da rundunar ta yi.

Ya ce an kama ƴan daba 106 da waɗanda ake zargi masu fashi da makami ne su 25 da mutum biyu da ake zargi suna garkuwa da mutane sai masu satar mota uku da dillalan miyagun ƙwayoyi uku a sassa daban-daban na jihar.

“Mun kuma gano motoci biyu da babura takwas da wuƙaƙe 58 da bindiga ɗaya da ƙunshi 87 na abin da ake zargin tabar wiwi ne.

Kiyawa ya ce kamen ya biyo bayan shawagin da ƴan sanda suke yi a sassan jihar domin hana aikata laifuka.

A cewarsa, mutanen da aka kama na sashen binciken manyan laifuka na rundunar inda ake gudanar da bincike a kan su.

Kwamishinan ƴan sanda na jihar, Salman Dogo Garba ya ce rundunar za ta ci gaba da aiki ba dare ba rana domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp