Home General NDLEA ta Bukaci yin Gwajin shaye-shaye kafin Aure a jihar Kano

NDLEA ta Bukaci yin Gwajin shaye-shaye kafin Aure a jihar Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA reshen jihar Kano ta bukaci wajabta yin gwajin ta’ammali da miyagun kwayoyi kafin aure a jihar.

Kwamandan hukumar  Abubakar Idris Ahmad ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Alhamis.

“A yunkurin hukumar na dakile dabiar ta’ammali da miyagun kwayoyi ta gabatar da wannan gwaji don kawar da dabiar daga Nijeriya,” a cewar sa.

Idris Ahmad yace gwajin zai zama wani mataki na magance shan miyagun kwayoyin da kuma kare wadanda basu fara ba daga cikin ma’auratan gami da wayar da kai da fadakar da su hadarin fadawa harkokin shaye – shayen.

Ya ce samar da dokar zai taimaka matuka wajen magance yawan mutuwar aure, gami da rage yawan matan aure dake shiga harkokin shaye – shayen a jihar.

daga bisani kwamandan hukumar ya bukaci wata da matasa da su guji dabi’ar shaye – shaye tare da bata hadin kai don kawar da ta’adar daga jihar da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp