Home General NDLEA ta Bukaci yin Gwajin shaye-shaye kafin Aure a jihar Kano

NDLEA ta Bukaci yin Gwajin shaye-shaye kafin Aure a jihar Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA reshen jihar Kano ta bukaci wajabta yin gwajin ta’ammali da miyagun kwayoyi kafin aure a jihar.

Kwamandan hukumar  Abubakar Idris Ahmad ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Alhamis.

“A yunkurin hukumar na dakile dabiar ta’ammali da miyagun kwayoyi ta gabatar da wannan gwaji don kawar da dabiar daga Nijeriya,” a cewar sa.

Idris Ahmad yace gwajin zai zama wani mataki na magance shan miyagun kwayoyin da kuma kare wadanda basu fara ba daga cikin ma’auratan gami da wayar da kai da fadakar da su hadarin fadawa harkokin shaye – shayen.

Ya ce samar da dokar zai taimaka matuka wajen magance yawan mutuwar aure, gami da rage yawan matan aure dake shiga harkokin shaye – shayen a jihar.

daga bisani kwamandan hukumar ya bukaci wata da matasa da su guji dabi’ar shaye – shaye tare da bata hadin kai don kawar da ta’adar daga jihar da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp