Home DUNIYA NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda...

NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda ga Gwamnatin Zamfara

Babban ma shawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, ya hannunta mutane 16 da aka kubutar daga hannun masu garkuwa da mutane ga wakilan gwamnatin jihar Zamfara.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa da dabaru na cibiyar yaki da ýan ta’adda a ofishin mai babban mai shawarcin , NCTC – ONSA, a ranar alhamis a birnin tarayya Abuja.

Ribadu yace damka wadanda aka kubutar din na shaida kan yunkurin gwamnatin tarayya kan mabanbanta ceto wadanda masu garkuwa da mutane suka kama sannan ya nuna kokarin gwamnatin tarayyar Nijeriya na kare rayukan ýan Nijeriya da wadanda ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.

Yace an yi garkuwa da mutanen ne a kwaryar Zurmi, Duran da Gusau dake cikin garin Zamfara a ranar 22 ga watan Afrilu, wanda kuma atisayen da NCTC ya sami nasarar kubutar da su.

Ya bukaci al’umma Nijeirya da su cigaba da bawa jamián tsaro goyan baya domin cimma kudirin gwamnatin tarayya na kawar matsalolin tsaro a Nijeriya.

daga bisani kodinatan NTCT, Manjo Janar Adamu Laka ya bukaci al’umma dasu ke gaggauta sanar da Jami’an tsaro da zarar wani lamarin tsaro ya auku domin daukar mataki da wuri.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp