Home DUNIYA NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda...

NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda ga Gwamnatin Zamfara

Babban ma shawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, ya hannunta mutane 16 da aka kubutar daga hannun masu garkuwa da mutane ga wakilan gwamnatin jihar Zamfara.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa da dabaru na cibiyar yaki da ýan ta’adda a ofishin mai babban mai shawarcin , NCTC – ONSA, a ranar alhamis a birnin tarayya Abuja.

Ribadu yace damka wadanda aka kubutar din na shaida kan yunkurin gwamnatin tarayya kan mabanbanta ceto wadanda masu garkuwa da mutane suka kama sannan ya nuna kokarin gwamnatin tarayyar Nijeriya na kare rayukan ýan Nijeriya da wadanda ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.

Yace an yi garkuwa da mutanen ne a kwaryar Zurmi, Duran da Gusau dake cikin garin Zamfara a ranar 22 ga watan Afrilu, wanda kuma atisayen da NCTC ya sami nasarar kubutar da su.

Ya bukaci al’umma Nijeirya da su cigaba da bawa jamián tsaro goyan baya domin cimma kudirin gwamnatin tarayya na kawar matsalolin tsaro a Nijeriya.

daga bisani kodinatan NTCT, Manjo Janar Adamu Laka ya bukaci al’umma dasu ke gaggauta sanar da Jami’an tsaro da zarar wani lamarin tsaro ya auku domin daukar mataki da wuri.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp