Home DUNIYA NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda...

NSA ta mika mutum 16 da aka kubutar da hanun ‘yan Ta’adda ga Gwamnatin Zamfara

Babban ma shawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, ya hannunta mutane 16 da aka kubutar daga hannun masu garkuwa da mutane ga wakilan gwamnatin jihar Zamfara.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da shugaban sashen sadarwa da dabaru na cibiyar yaki da ýan ta’adda a ofishin mai babban mai shawarcin , NCTC – ONSA, a ranar alhamis a birnin tarayya Abuja.

Ribadu yace damka wadanda aka kubutar din na shaida kan yunkurin gwamnatin tarayya kan mabanbanta ceto wadanda masu garkuwa da mutane suka kama sannan ya nuna kokarin gwamnatin tarayyar Nijeriya na kare rayukan ýan Nijeriya da wadanda ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.

Yace an yi garkuwa da mutanen ne a kwaryar Zurmi, Duran da Gusau dake cikin garin Zamfara a ranar 22 ga watan Afrilu, wanda kuma atisayen da NCTC ya sami nasarar kubutar da su.

Ya bukaci al’umma Nijeirya da su cigaba da bawa jamián tsaro goyan baya domin cimma kudirin gwamnatin tarayya na kawar matsalolin tsaro a Nijeriya.

daga bisani kodinatan NTCT, Manjo Janar Adamu Laka ya bukaci al’umma dasu ke gaggauta sanar da Jami’an tsaro da zarar wani lamarin tsaro ya auku domin daukar mataki da wuri.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp