Home General Kotun tarayya ta rushe kwamitin dake bincikar Ganduje a Kano

Kotun tarayya ta rushe kwamitin dake bincikar Ganduje a Kano

Mai shari’a Simon Amobeda na babbar kotun tarayya dake zaman ta a Kano, ya baiwa Justis Faruk Adamu da Mai shari’a Zuwaira Yusuf, alkalan babbar kotun jihar Kano wa’adin sa’o’i 48 da su yi murabus daga shugabancin kwamitin binciken almundahana da kadarorin gwamnati da kuma tashe-tashen hankula na siyasa, wadanda gwamnatin jihar kano ta kafa.

Da yake yanke hukunci a ranar Alhamis a karar da tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya shigar, mai shari’a Amobeda, ya ce hukumar ta kula da harkokin Shari’a ta kasa zata dakatar da biyan duk wani albashi da alawus-alawus da ake yi biyan alkalan biyu daga hadakar asusun shigarta idan har suka gaza bi umarnin kotun.

idan za’a iya tunawa a ranar 4 ga watan Afrilu ne Gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf, ya kaddamar da kwamitocin binciken shari’ar guda biyu karkashin jagorancin Mai Shari’a Adamu da Yusuf, domin gudanar da bincike a kan almubazzaranci da dukiyar jama’a, tashe-tashen hankulan siyasa da kuma wadanda suka bace daga shekarar 2015 zuwa yanzu. 2023.

Mai shari’a Amobeda ya bayar da umarnin cewa alkalan su daina gudanar da ayyukan zartarwa da gwamnan ya ba su a cikin kotuna wanda ke nufin yanke hukunci a tsakanin mutane da hukumomi a jihar.

Kotun ta kuma bayyana cewa gwamnan ba shi da hurumin nadawa da kuma rantsar da su a matsayin shugabannin hukumar bincike, ofishin da ya kamata kwamishinoni su gudanar da shi.

Kotun ta kuma bayyana cewa, duba da hukuncin da Mai shari’a Abdullahi Muhammad Liman ya yanke na cewa EFCC da ICPC ne kawai za su iya bincikar tsohon gwamnan, ya ce abun da gwamnan ya yi na kafa kwamitin da zai binciki tsohuwar gwamnatin mai kara cin fuska ne a ga alfarmar bangaren Shari’a.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp