Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya sabon firaministan Birtaniya Sir Keir Starmer, murnar kama aiki, bayan nasarar da jam’iyyarsa ta yi a zaɓen ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban na Najeriya, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce a matsayin Tinubu na tsohon jigon adawa a Najeriya, ya san yadda sabon firaministan ke da ƙwarin gwiwa kan sabon aikin da ya kama.

”Shekarun da ya kwashe yana jagorantar jam’iyyar hamayya sun ba shi damar sake shiryawa domin sake karɓar iko”, in ji Tinubu.

Shugaban na Najeriya ya ce yadda jam’iyyar ta yi shirin ta kuma sake karɓar mulki bayan shekara 14 ya nuna yadda mista Starmer ke da kyawawan halaye da ɗabi’u na shugabanci.

Shugaba Tinubu ya kuma ce a shirye Najeriya take don yin aiki tare da sabon firaministan don ƙara yauƙaƙa danƙon zumunci da ƙarfafa dimokraɗiyya da kasuwanci da ci gaba tsakanin ƙasashen biyu.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 14 hours 32 minutes 20 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 16 hours 13 minutes 45 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com