Home DUNIYA Zanga-Zaga -EFCC ta girke Jami’an Tsaro a Ofishinta dake jihar Legas

Zanga-Zaga -EFCC ta girke Jami’an Tsaro a Ofishinta dake jihar Legas

Hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arziki kasa ta’annati ta EFCC ta girke jami’an tsaro a bakin ofishinta na jihar legas bisa zargin gudanar da zanga – zanga kan hukumar.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito cewa an hangi wasu dakarun kai daukin gaggawa a bakin kofar shiga hukumar take yaki da masu zagon kasar ga tattalin arziki, cikin su kuwa har da jami’an tsaro DSS wadanda suka rufe dukkan hanyoyin shiga ofishin dake hanyar Awolowo dake yankin Ikoyi a jihar.

wannan dai na zuwa ne bayan hukumar ta fallasa wani shiri na wasu gungun mutane dake shirin gudanar da zanga-zanga a kanta.

A ranar Alhamis din data gabata mai magana da yawun hukumar Dele Oyewale, yace bayanan sirri sun tabbatar musu da cewa an shirya gudanar da zanga – zanga kan hukumar wanda kuma tsohon Gwamnan jihar da wasu tsuffin minitoci suke da alhakin hadata kan hukumar ta EFCC.

wani mai anfani da shafin X #PidomNigeria shine ya fara yada wani sako ta cikin wata takar dar sanarwa wanda ya yi mata adreshi zuwa ga shugaban hukumar, Ola Olukoyode a shafin dake bukatar matasa su fito ayi zanga zanga  a cikin dare 4 ga watan Yunin 2023.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp