Home DUNIYA Zanga-Zaga -EFCC ta girke Jami’an Tsaro a Ofishinta dake jihar Legas

Zanga-Zaga -EFCC ta girke Jami’an Tsaro a Ofishinta dake jihar Legas

Hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arziki kasa ta’annati ta EFCC ta girke jami’an tsaro a bakin ofishinta na jihar legas bisa zargin gudanar da zanga – zanga kan hukumar.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito cewa an hangi wasu dakarun kai daukin gaggawa a bakin kofar shiga hukumar take yaki da masu zagon kasar ga tattalin arziki, cikin su kuwa har da jami’an tsaro DSS wadanda suka rufe dukkan hanyoyin shiga ofishin dake hanyar Awolowo dake yankin Ikoyi a jihar.

wannan dai na zuwa ne bayan hukumar ta fallasa wani shiri na wasu gungun mutane dake shirin gudanar da zanga-zanga a kanta.

A ranar Alhamis din data gabata mai magana da yawun hukumar Dele Oyewale, yace bayanan sirri sun tabbatar musu da cewa an shirya gudanar da zanga – zanga kan hukumar wanda kuma tsohon Gwamnan jihar da wasu tsuffin minitoci suke da alhakin hadata kan hukumar ta EFCC.

wani mai anfani da shafin X #PidomNigeria shine ya fara yada wani sako ta cikin wata takar dar sanarwa wanda ya yi mata adreshi zuwa ga shugaban hukumar, Ola Olukoyode a shafin dake bukatar matasa su fito ayi zanga zanga  a cikin dare 4 ga watan Yunin 2023.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp