Home DUNIYA Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya sabon firaministan Birtaniya Sir Keir Starmer, murnar kama aiki, bayan nasarar da jam’iyyarsa ta yi a zaɓen ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban na Najeriya, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce a matsayin Tinubu na tsohon jigon adawa a Najeriya, ya san yadda sabon firaministan ke da ƙwarin gwiwa kan sabon aikin da ya kama.

”Shekarun da ya kwashe yana jagorantar jam’iyyar hamayya sun ba shi damar sake shiryawa domin sake karɓar iko”, in ji Tinubu.

Shugaban na Najeriya ya ce yadda jam’iyyar ta yi shirin ta kuma sake karɓar mulki bayan shekara 14 ya nuna yadda mista Starmer ke da kyawawan halaye da ɗabi’u na shugabanci.

Shugaba Tinubu ya kuma ce a shirye Najeriya take don yin aiki tare da sabon firaministan don ƙara yauƙaƙa danƙon zumunci da ƙarfafa dimokraɗiyya da kasuwanci da ci gaba tsakanin ƙasashen biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp