Home DUNIYA Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Tinubu ya taya Starmer murnar zama sabon Firaministan Birtaniya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya sabon firaministan Birtaniya Sir Keir Starmer, murnar kama aiki, bayan nasarar da jam’iyyarsa ta yi a zaɓen ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban na Najeriya, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce a matsayin Tinubu na tsohon jigon adawa a Najeriya, ya san yadda sabon firaministan ke da ƙwarin gwiwa kan sabon aikin da ya kama.

”Shekarun da ya kwashe yana jagorantar jam’iyyar hamayya sun ba shi damar sake shiryawa domin sake karɓar iko”, in ji Tinubu.

Shugaban na Najeriya ya ce yadda jam’iyyar ta yi shirin ta kuma sake karɓar mulki bayan shekara 14 ya nuna yadda mista Starmer ke da kyawawan halaye da ɗabi’u na shugabanci.

Shugaba Tinubu ya kuma ce a shirye Najeriya take don yin aiki tare da sabon firaministan don ƙara yauƙaƙa danƙon zumunci da ƙarfafa dimokraɗiyya da kasuwanci da ci gaba tsakanin ƙasashen biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp