Home DUNIYA Rumbun wutar lantarkin Najeriya ya sake ɗaukewa a karo na 4 cikin...

Rumbun wutar lantarkin Najeriya ya sake ɗaukewa a karo na 4 cikin 2024

Kamfanin Dakon Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya tabbatar da sake ɗaukewar wutar lantarki daga rumbun samar da ita na Najeriya a ranar Asabar.

Wannan dai shi ne karo na huɗu da wutar ta ke ɗaukewa gaba ɗaya tun daga farkon wannan shekarar zuwa yanzu.

Wani rahoto da kamfanin ya wallafa a shafinsa na internet ya nuna cewa da misalin karfe 2:00 na yammacin wannan rana an iya samar da wutar da yawanta ya kai megawat 2,797.16, kasa da yadda ake samu a baya, idan an kwatanta da misalin karfe 1:00 na wannan yammaci da ya kai megawatt 3,417.99.

Haka adadin wutar ya sake saka da misalign karfe 3 na yammacin zuwa 1,020.08 inda daga bisani cikin mamaki ya koma 0.80 da karfe.

Ba tun yanzu ba ’yan Najeriya ke kokawa kan yadda rashin wutar lantarki ke haifar musu da tasgaro a harkokin su na yau da kullum.

A bana kaɗai, kasar nan ta fuskanci durkushewar wutar lantarki akalla sau uku, inda matsalar ta faru sau 227 a tsahon shekaru 14 kamar yadda kamfanin dakon wutar lantarkin na TCN ya bayyana.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp