Home DUNIYA Kada ku bari ’yan ta’adda su kassara zaman lafiyar kasar nan –...

Kada ku bari ’yan ta’adda su kassara zaman lafiyar kasar nan – Tinubu ga sojoji

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci dakarun sojoji da kada su bari ’yan ta’adda su ga bayan al’ummar Nijeriya.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a wani bangare na bikin da rundunar sojin ta gudanar a barikin sojoji na uku da ke Rukuba a Karamar Hukumar Bassa a jihar Filato.

Tinubu wanda ya sami wakilcin Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce wajibi dakarun su kare rayukan ’yan kasar a gidaje ko kuma a wuraren mu’amalarsu na yau da kullum.

da yake bayani tun da farko, Babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya ce sojojin kasar nan kwararru ne tsahon shekaru 161.

Nijeriya dai na fama da matsalolin rashin tsaro wacce ta addabi Arewacin kasar, yayin da na kudanci ke fama da matsaloli barayin mai da masu kokarin ficewa daga ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp