Home DUNIYA Rumbun wutar lantarkin Najeriya ya sake ɗaukewa a karo na 4 cikin...

Rumbun wutar lantarkin Najeriya ya sake ɗaukewa a karo na 4 cikin 2024

Kamfanin Dakon Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya tabbatar da sake ɗaukewar wutar lantarki daga rumbun samar da ita na Najeriya a ranar Asabar.

Wannan dai shi ne karo na huɗu da wutar ta ke ɗaukewa gaba ɗaya tun daga farkon wannan shekarar zuwa yanzu.

Wani rahoto da kamfanin ya wallafa a shafinsa na internet ya nuna cewa da misalin karfe 2:00 na yammacin wannan rana an iya samar da wutar da yawanta ya kai megawat 2,797.16, kasa da yadda ake samu a baya, idan an kwatanta da misalin karfe 1:00 na wannan yammaci da ya kai megawatt 3,417.99.

Haka adadin wutar ya sake saka da misalign karfe 3 na yammacin zuwa 1,020.08 inda daga bisani cikin mamaki ya koma 0.80 da karfe.

Ba tun yanzu ba ’yan Najeriya ke kokawa kan yadda rashin wutar lantarki ke haifar musu da tasgaro a harkokin su na yau da kullum.

A bana kaɗai, kasar nan ta fuskanci durkushewar wutar lantarki akalla sau uku, inda matsalar ta faru sau 227 a tsahon shekaru 14 kamar yadda kamfanin dakon wutar lantarkin na TCN ya bayyana.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp