Home DUNIYA Sojoji na son mutanen Zamfara su rika ba su bayanai don dakile...

Sojoji na son mutanen Zamfara su rika ba su bayanai don dakile ta’addanci

Babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Laftanar-Janar Taoored Lagbaja, ya bukaci al’ummar jihar Zamfara da su rika ba dakarunsu bayanan da za su taimaka musu wajen gano maboyar ’yan ta’addaa jihar.

Lagbaja ya bayyana hakan ne ta bakin kwamandan runduna ta daya da ke garin Gusau, babban birnin jihar.

Kazalika, Babban Hafsan Sojojin ya raba kayan karatu da na sawa ga masu karamin karfi..

Shi ma da yake jawabi a yayin taron, Kwamandan rundunar ta daya wanda ya sami wakilcin Kanal Joseph Umaru, ya ce sun raba kayan ne domin tallafa wa dalibai da kuma masu karamin karfin domin karfafa musu gwiwa a fannin ilimi.

Ya kara da cewa wannan tallafi na matsayin wani bangare na ranar bikin Ranar Sojojin da aka gudanar a jihar wanda ya kunshi ayyukan rundunar da kuma tabbatar da hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp