Home DUNIYA Tinubu ya kafa sabuwar ma’aikatar harkokin kiwo a Nijeriya

Tinubu ya kafa sabuwar ma’aikatar harkokin kiwo a Nijeriya

Shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad Tinubu ya kafa sabuwar Ma’aikatar Harkokin Kiwon Dabbobi a Nijeriya.

wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake tsaka da rikici a zauren majalisar kasar kan yadda makiyaya zasu gudanar da harkokin kiwo a kasar.

Bola Tinubu ya sanar da hakan ne lokacin da ya ke kaddamar da kwamitin da zai gyara tsarin kiwo, Kwamitin da zai yi aiki wajen magance matsaloli tsakanin manoma da makiyaya,

A taron da ya sami halartar, mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, da kuma wasu jami’an gwamnati.

A watan Satumban 2023, Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin shugaban ƙasa don gyaran bangaren kiwo da magance rikice-rikicen makiyaya da manoma.

Wannan shawarar ta biyo bayan rahoton taron kasa kan gyara tsarin kiwo da rage rikice-rikicen da ke da nasaba da kiwo a Najeriya.
Kungiyar Miyetti Allah ta MACBAN, ta buƙace shugaban ƙasa ya ƙirƙiro ma’aikatar kiwo.

Shugabansu, Alhaji Baba Usman Ngelzarma, ya ce makiyaya na buƙatar ma’aikata mai zaman kanta da za ta kula da dukkanin al’amuran da suka shafi kiwo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp