Home DUNIYA Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba zata lamunci ayyukan garkuwa...

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba zata lamunci ayyukan garkuwa a jihar ba

Rundunar ‘Yan sandan jihar Kano ta sami nasarar ceto wata ƙaramar yarinya mai kimanin shekara biyu da rabi, bayan wani Makocinsu yayi garkuwa da ita harya nemi kuɗin fansar Naira Miliyan 2 a wurin iyayenta.
wannan na kunshe ta cikin wata sanarwar da Jami’in hulda da Jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, inda tace, tuni wanda ake zargin ya amsa laifin sa harma ya kai Jami’an rundunar wurin da ya ɓoye yarinyar.
Lamarin ya faru ne unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka dake ƙaramar hukumar Kumbotso, inda matashin me suna Zakariyya Muhammad ɗan kimanin Shekaru 22 ya sace yarinyar me suna Amina.
Haka kuma rundunar ta kai yarinyar Asibitin ƙwararru na Murtala Muhammed dake Kano, inda aka bata kulawar gaggawa wanda tuni aka sallame ta.
Kwamishinan ‘yansandan jihar CP Salman Dogo Garba ya ce rundunar ba zata lamunci irin waɗannan ayyukan ba, a inda ya jaddada cewa zasu saka ƙafar wando ɗaya da masu yunƙurin aikata muggan laifuka a jihar.
daga bisani rundunar ta yaba da yadda al’ummar jihar suke bin doka da oda, harma ta buƙaci mutane su ci-gaba da sanya idanu a yankunan su domin bada gudunmawar kakkaɓe dukkan wasu ɓata gari a fadin jihar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp