Home DUNIYA Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba zata lamunci ayyukan garkuwa...

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba zata lamunci ayyukan garkuwa a jihar ba

Rundunar ‘Yan sandan jihar Kano ta sami nasarar ceto wata ƙaramar yarinya mai kimanin shekara biyu da rabi, bayan wani Makocinsu yayi garkuwa da ita harya nemi kuɗin fansar Naira Miliyan 2 a wurin iyayenta.
wannan na kunshe ta cikin wata sanarwar da Jami’in hulda da Jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, inda tace, tuni wanda ake zargin ya amsa laifin sa harma ya kai Jami’an rundunar wurin da ya ɓoye yarinyar.
Lamarin ya faru ne unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka dake ƙaramar hukumar Kumbotso, inda matashin me suna Zakariyya Muhammad ɗan kimanin Shekaru 22 ya sace yarinyar me suna Amina.
Haka kuma rundunar ta kai yarinyar Asibitin ƙwararru na Murtala Muhammed dake Kano, inda aka bata kulawar gaggawa wanda tuni aka sallame ta.
Kwamishinan ‘yansandan jihar CP Salman Dogo Garba ya ce rundunar ba zata lamunci irin waɗannan ayyukan ba, a inda ya jaddada cewa zasu saka ƙafar wando ɗaya da masu yunƙurin aikata muggan laifuka a jihar.
daga bisani rundunar ta yaba da yadda al’ummar jihar suke bin doka da oda, harma ta buƙaci mutane su ci-gaba da sanya idanu a yankunan su domin bada gudunmawar kakkaɓe dukkan wasu ɓata gari a fadin jihar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp