Home DUNIYA Tinubu ya kafa sabuwar ma’aikatar harkokin kiwo a Nijeriya

Tinubu ya kafa sabuwar ma’aikatar harkokin kiwo a Nijeriya

Shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad Tinubu ya kafa sabuwar Ma’aikatar Harkokin Kiwon Dabbobi a Nijeriya.

wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake tsaka da rikici a zauren majalisar kasar kan yadda makiyaya zasu gudanar da harkokin kiwo a kasar.

Bola Tinubu ya sanar da hakan ne lokacin da ya ke kaddamar da kwamitin da zai gyara tsarin kiwo, Kwamitin da zai yi aiki wajen magance matsaloli tsakanin manoma da makiyaya,

A taron da ya sami halartar, mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, da kuma wasu jami’an gwamnati.

A watan Satumban 2023, Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin shugaban ƙasa don gyaran bangaren kiwo da magance rikice-rikicen makiyaya da manoma.

Wannan shawarar ta biyo bayan rahoton taron kasa kan gyara tsarin kiwo da rage rikice-rikicen da ke da nasaba da kiwo a Najeriya.
Kungiyar Miyetti Allah ta MACBAN, ta buƙace shugaban ƙasa ya ƙirƙiro ma’aikatar kiwo.

Shugabansu, Alhaji Baba Usman Ngelzarma, ya ce makiyaya na buƙatar ma’aikata mai zaman kanta da za ta kula da dukkanin al’amuran da suka shafi kiwo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp