Home DUNIYA An kama mai garkuwa da mutane a wajen karbar kudin fansa a Yobe

An kama mai garkuwa da mutane a wajen karbar kudin fansa a Yobe

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe dake arewa maso gabashin Nijeriya ta tabbatar da kama Usman Garba mai kimanin shekaru 30 da take zargi da ayyukan garkuwa da mutane a jihar.

Kakakin rundunar, DSP Dungus Abdulkarim ne ya bayyana hakan, inda yace a ranar 5 ga watan Yunin shekarar 2024 da misalin karfe 1 na yamma, jami’ai daga sashen (SID) suka sami nasarar kama Usman Garba dan Asalin kauyen Katarko dake karamar hukumar Gujba, a kan hanyar sa ta zuwa kashe kason da ya samu a wata garkuwa da suka gudanar.

”Wanda ake zargin guda ne cikin mabobin wata tawaga da suka kware wajen fashi  da makami, garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa da kuma satar shanu a karamar hukumar hukumar Gujba da garuruwan dake makotaka da garin.

”Tawagar suke da alhakin garkuwar da akayi baya-bayannan a wani wurin zaman fulani da ake kira da Babaram Muktum a karamar hukumar ta Gujba, inda suka yi garkuwa tare da karbar kudin fansa naira miliyan 1 da dubu dari 6.

“sauran mambobin kungiyar sun tsere, amma rundunar na kokari domin tabbatar da ta kamasu.”

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp