Home DUNIYA Kamfanonin jaragen Sama da ke saba ka’idoji za su fuskanci hukunci mai...

Kamfanonin jaragen Sama da ke saba ka’idoji za su fuskanci hukunci mai tsanani – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya, NCAA ta yi gargaɗin cewa za ta hukunta kamfanonin sufurin da ke yaudarar matafiya a kan lokacin tafiyar jirage.

Mukaddashin daraktan hukumar, Chris Najomo ne ya bayyana hakan inda ya ce hukumar ba za ta lamunci rashin cika alƙawari da kuma kiyaye ƙa’idojin sufurin jirgin sama ba.

Ya yi gargaɗin cewa kamfanonin da suke saba ka’idojin za su fuskanci hukunci mai tsanani, kamar yadda doka ta yi tanadi.

Hukumar ta ce ta yi tanadi mai inganci domin sauƙaƙe yadda ake mallakar lasisin gudanar da kamfanonin jiragen sama a Najeriya, da kuma kaucewa kura-kuran baya.

“NCAA ta na fatan ganin hakan zai sa kamfanonin jiragen su tashi tsaye domin gudanar da ayyukan su yadda ya dace” inji Chris Najomo.

NCAA ta jaddada cewa babu wani dalili da zai hana kamfanonin jiragen sama gudanar da ayyukan cikin tsari kamar yadda ake yi a sauran ƙasashen duniya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp