Home DUNIYA NERC tace ya zama dole ta hukunta kamfanonin rarraba lantarki a Najeriya

NERC tace ya zama dole ta hukunta kamfanonin rarraba lantarki a Najeriya

Hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya NERC, ta gargadi kamfanonin rarraba wutar lantarki (DisCos) da cewa za su fuskanci hukunci idan ba su yi amfani da aƙalla kashi 95 cikin 100 na makamashin da aka ware musu domin samar da wutar lantarki ga jama’a a kowanne wata ba.

Wannan wani ɓangare ne na sabon umarnin hukumar NERC kan tsarin sa ido kan ayyuka rarraba wutar lantarkin.

Hukumar ta ce duk kamfanin rarraba wutar lantarki da ya kasa cika wannan ƙofa na samar da wuta zai ga raguwar kashi 5 cikin 100 a cikin kuɗin gudanarwa da ayyukan su na kwata na gaba.

NERC ta gabatar da ma’auni bakwai masu mahimmanci (KPIs) don tantance ayyukan kamfanonin.

NERC ta jaddada cewa hukunta kamfanonin ya zama dole don kiyaye tsarin kasuwa da ɗorewar kudi.

Hukumar ta kuma ce rashin mayar da hankali da kuma martani a kan ƙorafe-ƙorafen mabuƙaci zai haifar da cin tara a kullum daga ₦1,000 zuwa 10,000.

NERC ta ƙarar da cewa rashin bin ka’ida na kuma iya haifar da korar jami’an da ke da alhaki.

Shugaban NERC, Sanusi Garba, ya sanya hannu kan wannan umarni ne a ranar 5 ga Yulin 2024, inda ya jaddada ƙudirin hukumar na tabbatar da tsauraran matakan tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp