Home DUNIYA NERC tace ya zama dole ta hukunta kamfanonin rarraba lantarki a Najeriya

NERC tace ya zama dole ta hukunta kamfanonin rarraba lantarki a Najeriya

Hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya NERC, ta gargadi kamfanonin rarraba wutar lantarki (DisCos) da cewa za su fuskanci hukunci idan ba su yi amfani da aƙalla kashi 95 cikin 100 na makamashin da aka ware musu domin samar da wutar lantarki ga jama’a a kowanne wata ba.

Wannan wani ɓangare ne na sabon umarnin hukumar NERC kan tsarin sa ido kan ayyuka rarraba wutar lantarkin.

Hukumar ta ce duk kamfanin rarraba wutar lantarki da ya kasa cika wannan ƙofa na samar da wuta zai ga raguwar kashi 5 cikin 100 a cikin kuɗin gudanarwa da ayyukan su na kwata na gaba.

NERC ta gabatar da ma’auni bakwai masu mahimmanci (KPIs) don tantance ayyukan kamfanonin.

NERC ta jaddada cewa hukunta kamfanonin ya zama dole don kiyaye tsarin kasuwa da ɗorewar kudi.

Hukumar ta kuma ce rashin mayar da hankali da kuma martani a kan ƙorafe-ƙorafen mabuƙaci zai haifar da cin tara a kullum daga ₦1,000 zuwa 10,000.

NERC ta ƙarar da cewa rashin bin ka’ida na kuma iya haifar da korar jami’an da ke da alhaki.

Shugaban NERC, Sanusi Garba, ya sanya hannu kan wannan umarni ne a ranar 5 ga Yulin 2024, inda ya jaddada ƙudirin hukumar na tabbatar da tsauraran matakan tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp