Home DUNIYA An kama mai garkuwa da mutane a wajen karbar kudin fansa a Yobe

An kama mai garkuwa da mutane a wajen karbar kudin fansa a Yobe

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe dake arewa maso gabashin Nijeriya ta tabbatar da kama Usman Garba mai kimanin shekaru 30 da take zargi da ayyukan garkuwa da mutane a jihar.

Kakakin rundunar, DSP Dungus Abdulkarim ne ya bayyana hakan, inda yace a ranar 5 ga watan Yunin shekarar 2024 da misalin karfe 1 na yamma, jami’ai daga sashen (SID) suka sami nasarar kama Usman Garba dan Asalin kauyen Katarko dake karamar hukumar Gujba, a kan hanyar sa ta zuwa kashe kason da ya samu a wata garkuwa da suka gudanar.

”Wanda ake zargin guda ne cikin mabobin wata tawaga da suka kware wajen fashi  da makami, garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa da kuma satar shanu a karamar hukumar hukumar Gujba da garuruwan dake makotaka da garin.

”Tawagar suke da alhakin garkuwar da akayi baya-bayannan a wani wurin zaman fulani da ake kira da Babaram Muktum a karamar hukumar ta Gujba, inda suka yi garkuwa tare da karbar kudin fansa naira miliyan 1 da dubu dari 6.

“sauran mambobin kungiyar sun tsere, amma rundunar na kokari domin tabbatar da ta kamasu.”

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp