Home DUNIYA An kama mai garkuwa da mutane a wajen karbar kudin fansa a Yobe

An kama mai garkuwa da mutane a wajen karbar kudin fansa a Yobe

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe dake arewa maso gabashin Nijeriya ta tabbatar da kama Usman Garba mai kimanin shekaru 30 da take zargi da ayyukan garkuwa da mutane a jihar.

Kakakin rundunar, DSP Dungus Abdulkarim ne ya bayyana hakan, inda yace a ranar 5 ga watan Yunin shekarar 2024 da misalin karfe 1 na yamma, jami’ai daga sashen (SID) suka sami nasarar kama Usman Garba dan Asalin kauyen Katarko dake karamar hukumar Gujba, a kan hanyar sa ta zuwa kashe kason da ya samu a wata garkuwa da suka gudanar.

”Wanda ake zargin guda ne cikin mabobin wata tawaga da suka kware wajen fashi  da makami, garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa da kuma satar shanu a karamar hukumar hukumar Gujba da garuruwan dake makotaka da garin.

”Tawagar suke da alhakin garkuwar da akayi baya-bayannan a wani wurin zaman fulani da ake kira da Babaram Muktum a karamar hukumar ta Gujba, inda suka yi garkuwa tare da karbar kudin fansa naira miliyan 1 da dubu dari 6.

“sauran mambobin kungiyar sun tsere, amma rundunar na kokari domin tabbatar da ta kamasu.”

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp