Majalisar wakilai ta kafa kwamitin bincike kan hukumar NAHCON

Majalisar wakilan Nijeriya ta kafa kwamiti domin bincikar hukumar jin dadin alhazai ta kasar, bisa yadda ta gudanar da ayyukan hajin shekarar 2024.

Wannan dai na zuwa ne bayan kudirin da dan majlisar mai wakiltar al’ummar mazabar Barutai/Kaigama, Muhammad Bio daga jihar Kwara ya gabatar a gaban majalisar yayin zamanta na ranar talata.

biyo bayan kudirin majalisar tayi fatali da yadda hukumar ta kasa da kuma ta birnin tarayya Abuja ta gudanar da aikin hajjin na shekarar 2024, don haka ta kafa kwamitin da zai bincika wakilan hukumar a hajjin.

tuni dai kakakin majalisar wakilan Tajuddeen Abbas, ya ayyana mamba dake wakiltar Alúmmar mazabar Jibia/kaita daga Jihar Katsina, Sada Soli matsayin shugaban kwamitin.

an yi wa kudirin take, ” gaggauta bincike akan hukumar jin dadin alhazai ta NAHCON ta kasa da kuma ta birnin tarayya Abuja, Wakilansu, bisa birinburin a shirin gudanar da ayyukan sauke farali na shekarar 2024,”

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 15 minutes 12 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 56 minutes 37 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com