Home DUNIYA Majalisar wakilai ta kafa kwamitin bincike kan hukumar NAHCON

Majalisar wakilai ta kafa kwamitin bincike kan hukumar NAHCON

Majalisar wakilan Nijeriya ta kafa kwamiti domin bincikar hukumar jin dadin alhazai ta kasar, bisa yadda ta gudanar da ayyukan hajin shekarar 2024.

Wannan dai na zuwa ne bayan kudirin da dan majlisar mai wakiltar al’ummar mazabar Barutai/Kaigama, Muhammad Bio daga jihar Kwara ya gabatar a gaban majalisar yayin zamanta na ranar talata.

biyo bayan kudirin majalisar tayi fatali da yadda hukumar ta kasa da kuma ta birnin tarayya Abuja ta gudanar da aikin hajjin na shekarar 2024, don haka ta kafa kwamitin da zai bincika wakilan hukumar a hajjin.

tuni dai kakakin majalisar wakilan Tajuddeen Abbas, ya ayyana mamba dake wakiltar Alúmmar mazabar Jibia/kaita daga Jihar Katsina, Sada Soli matsayin shugaban kwamitin.

an yi wa kudirin take, ” gaggauta bincike akan hukumar jin dadin alhazai ta NAHCON ta kasa da kuma ta birnin tarayya Abuja, Wakilansu, bisa birinburin a shirin gudanar da ayyukan sauke farali na shekarar 2024,”

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp