Sojojin Nijeriya sun kama masu garkuwa da mutane 3 a jihar Taraba

Sojojin Nijeriya karkashin dakarun Operation WHIRL STROKE (OPWS) sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa a tsaunin Adamu Katibu dake karamar hukumar Lau ta jihar Taraba.

Wannan na matsayin matakin da rundunar ke dauka na kawar da ayyukan ta’addanci da suka addabi sassan kasar.

atisayen ya gudanane bayan wasu bayanan sirri da dakarun suka samu, hadin gwiwa da wasu dakarun tsaro a kasar, kan maboyar ta ‘yan ta’addan a yankin, inda suka yi musayar wuta daga bisani wasu cikin su suka tsere.

sai dai dakarun sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda uku daga cikin su, wadanda suka hadar da Haruna Buba mai kimanin shekaru (20), Hassan kakale mai shekaru da Hussaini kakale dukkansu masu shekaru (28) da haihuwa.

a yayin atisayen dakarun sun sami nasarar kubutar da Hauwa’u Alhaji Umaru da kuma Asma’u Alhaji Umaru da suka yi garkuwa da su tun a ranar 7 ga watan Yunin 2024, wanda tuni an kai su shalkwatar dakarun sojin dake ta 6 Brigade domin duba lafiyar su inda daga bisani za’a mika su ga ahlinsu.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 5 minutes 54 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 47 minutes 19 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com