Home DUNIYA Gini mai hawa 2 ya hallaka dalibai 16 a jihar Filato

Gini mai hawa 2 ya hallaka dalibai 16 a jihar Filato

Aƙalla ɗalibai 16 ne suka mutu bayan ruftawar ginin mai hawa biyu a wata makaranta a birnin Jos na jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya ranar Juma’a da safe.

Rahotonni sun ce ɗalibai masu yawa ne suka jikkata, yayin da ɗaliban da malamai suka maƙale a cikin ginin.

Ginin na makarantar Saint Academy – da ke unguwar Busa-buji a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa – ya rufta ne a lokacin da ɗaliban ke ɗaukar darussa.

Iyayen yara sun cika harabar makarantar bayan faruwar lamarin, domin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki, yayin da waɗanda suka ga gawarwakin ‘ya’yansu suka kiɗime.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya (NEMA) na ci gaba da aikin ceto domin zaƙulo sauran mutanen da ginin ya danne.

Kawo yanzu an gano gawargwaki aƙalla 16, to sai dai har yanzu ba a san adadin mutanen da suka mutu ba.

Akwai dai fiye da ɗalibai 1,000 a makarantar. Kawo yanzu dai ba a san dalilin da ya haddasa ruftawar ginin ba

Iyayen ɗalibai sun garzaya asibitin birnin Jos domin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Likitoci na kira ga al’umma su bayar da gudunmowar jini domin ceto rayukan ɗaliban da aka kai asibitin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp