Gini mai hawa 2 ya hallaka dalibai 16 a jihar Filato

Aƙalla ɗalibai 16 ne suka mutu bayan ruftawar ginin mai hawa biyu a wata makaranta a birnin Jos na jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya ranar Juma’a da safe.

Rahotonni sun ce ɗalibai masu yawa ne suka jikkata, yayin da ɗaliban da malamai suka maƙale a cikin ginin.

Ginin na makarantar Saint Academy – da ke unguwar Busa-buji a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa – ya rufta ne a lokacin da ɗaliban ke ɗaukar darussa.

Iyayen yara sun cika harabar makarantar bayan faruwar lamarin, domin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki, yayin da waɗanda suka ga gawarwakin ‘ya’yansu suka kiɗime.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya (NEMA) na ci gaba da aikin ceto domin zaƙulo sauran mutanen da ginin ya danne.

Kawo yanzu an gano gawargwaki aƙalla 16, to sai dai har yanzu ba a san adadin mutanen da suka mutu ba.

Akwai dai fiye da ɗalibai 1,000 a makarantar. Kawo yanzu dai ba a san dalilin da ya haddasa ruftawar ginin ba

Iyayen ɗalibai sun garzaya asibitin birnin Jos domin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Likitoci na kira ga al’umma su bayar da gudunmowar jini domin ceto rayukan ɗaliban da aka kai asibitin.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 29 minutes 19 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 10 minutes 44 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com