Home DUNIYA Tinubu ya nada sabon shugaban Hukumar NPA

Tinubu ya nada sabon shugaban Hukumar NPA

Shugaban kasa Bola Tinubu ya naɗa Abubakar Ɗantsoho matsayin sabon Shugaban Hukumar Tashoshin Ruwa ta NPA.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Kasa, Ajuri Ngelale ya fitar a Yammacin Juma’ar.

Naɗin Ɗantsoho na zuwa ne bayan sallamar Mohammed Bello-Koko daga shugabancin hukumar tashoshin ruwa kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Kazalika, sanarwar ta ce Tinubu ya kuma naɗa tsohon Sanatan Ekiti ta Kudu kuma tsohon Ƙaramin Ministan Ayyuka, Dayo Adeyeye a matsayin sabon Shugaban Majalisar Gudanarwar hukumar ta NPA.

Kafin naɗinsa, Ɗantsoho ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar ciki har da muƙamin babban manaja ne hukumar ta NPA.

Dukkan su za su fara aiki ne nan take, kamar yadda sanarwar Fadar Shugaban Kasar ta bayyana.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp