Home DUNIYA Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba...

Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba – Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bazai saci dukiyar Al’ummar jihar kano ba, kuma bazai bari a satar musu kudi ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yammacin asabar yayin da yake kaddamar da kasha na biyu na rabon tallafi ga Al’ummar kananan hukumomi 44 dake fadin jihar nan.

Abba ya bayyana cewa gwamnatinsa baza ta saci kudin al’ummar jihar ba, sannan kuma zata dauki matakin hukunta dukkan wanda ya saci kudin a karkashin kulawarsa.

Gwamnan yace zasu raba miliyan 260 ga mata 5,200 wadanda suka fito daga kananan hukumomin jihar 44, wanda kowacce zata sami naira dubu 50, wanda zai taimakesu wajen sanya jari.

Haka kuma yace zasu cigaba da taimakawa matan dake kananan hukumomin da naira miliyan 260 a dukkanin wata har zuwa karshen wa’adin mulkin sa.

Yace wannan na cikin kudirin su da kuma abinda suka yi al’ummar jihar alkawari a yayin yakin neman zabe, kuma wannan na matsayin sakayya da zasu yiwa mata bisa gudunmawar da suka bayar wajen kafa gwamnatin.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp