Home DUNIYA Masarautar Kano ta tabbatar da tashin gobara a fadar sarki Muhammadu Sunusi...

Masarautar Kano ta tabbatar da tashin gobara a fadar sarki Muhammadu Sunusi II

Masarautar Kano ta tabbatar faruwar gobara da ake zargin kunnata aka yi a fadar Sarkin Kano na Malam Muhammadu Sanusi na biyu.

A sanarwar da shugaban ma’aikatan Sarkin Kano, Munnir Sanusi Abbas ya fitar a yammacin wannan rana ya ce wutar ta tashi ne a safiyar Asabar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, wutar wacce bata yi ɓarna mai yawa ba, ana kan binciken abinda ya haifar da ita.

A cewar sanarwar “Fadar na ɗaukar dukkan matakan da suka dace wajen tabbatar da tsaron fadar dama mutanen dake ciki, kuma tuni aka fara bincike don kaucewa tashin gobarar anan gaba”.

Tun da fari dai wani rahoto da ya fita a yammacin wannan rana ya ambaci rundunar ‘yan sanda jihar da tabbatar da aukuwar gobarar a fadar sarkin dake kofar kudu a gidan na rumfa.

Ko da dai itama rundunar bata ayyana musabban faruwar gobarar ba tace dai tana bincike ne kan abin da ya haddasa ta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp