Home DUNIYA Masarautar Kano ta tabbatar da tashin gobara a fadar sarki Muhammadu Sunusi...

Masarautar Kano ta tabbatar da tashin gobara a fadar sarki Muhammadu Sunusi II

Masarautar Kano ta tabbatar faruwar gobara da ake zargin kunnata aka yi a fadar Sarkin Kano na Malam Muhammadu Sanusi na biyu.

A sanarwar da shugaban ma’aikatan Sarkin Kano, Munnir Sanusi Abbas ya fitar a yammacin wannan rana ya ce wutar ta tashi ne a safiyar Asabar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, wutar wacce bata yi ɓarna mai yawa ba, ana kan binciken abinda ya haifar da ita.

A cewar sanarwar “Fadar na ɗaukar dukkan matakan da suka dace wajen tabbatar da tsaron fadar dama mutanen dake ciki, kuma tuni aka fara bincike don kaucewa tashin gobarar anan gaba”.

Tun da fari dai wani rahoto da ya fita a yammacin wannan rana ya ambaci rundunar ‘yan sanda jihar da tabbatar da aukuwar gobarar a fadar sarkin dake kofar kudu a gidan na rumfa.

Ko da dai itama rundunar bata ayyana musabban faruwar gobarar ba tace dai tana bincike ne kan abin da ya haddasa ta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp