Home DUNIYA Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kashe Trump

Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kashe Trump

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kisan tsohon shugaban Amurka, Donald Trump.

Trump wanda ke yin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Republican, ya tsallake rijiya da baya bayan an harbe shi, yana cikin jawabi a wajen yaƙin neman zaɓe, a Pennsylvania, lamarin da shugaban Najeriyan ya bayyana a matsayin babban tashin hankali.

Tinubu ya bi sahun sauran shugabannin duniya wajen bayyana takaici a kan harin, yana mai cewa irin wannan rikici bashi da mazauni a turbar dimokuraɗiyya.

A saƙon da Tinubu ya wallafa a shafin X yace harin da aka kai wa tsohon shugaban Amurka, Donald Trump babban abin tashin hankali ne kuma ya saɓawa turbar dimokuraɗiyya.

Sannan kuma ya miƙa jajen sa ga tsohon shugaban ƙasar, tare yi masa fatan samun sauki cikin sauri, gami da da mika ta’aziya ga ƴan uwan wanda ya mutu a harin.

Daga bisani Tinubu ya ce Najeriya tana tare da Amurka a wannan yanayi na alhini.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp