Home DUNIYA Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kashe Trump

Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kashe Trump

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kisan tsohon shugaban Amurka, Donald Trump.

Trump wanda ke yin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Republican, ya tsallake rijiya da baya bayan an harbe shi, yana cikin jawabi a wajen yaƙin neman zaɓe, a Pennsylvania, lamarin da shugaban Najeriyan ya bayyana a matsayin babban tashin hankali.

Tinubu ya bi sahun sauran shugabannin duniya wajen bayyana takaici a kan harin, yana mai cewa irin wannan rikici bashi da mazauni a turbar dimokuraɗiyya.

A saƙon da Tinubu ya wallafa a shafin X yace harin da aka kai wa tsohon shugaban Amurka, Donald Trump babban abin tashin hankali ne kuma ya saɓawa turbar dimokuraɗiyya.

Sannan kuma ya miƙa jajen sa ga tsohon shugaban ƙasar, tare yi masa fatan samun sauki cikin sauri, gami da da mika ta’aziya ga ƴan uwan wanda ya mutu a harin.

Daga bisani Tinubu ya ce Najeriya tana tare da Amurka a wannan yanayi na alhini.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp