Home DUNIYA Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kashe Trump

Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kashe Trump

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi allawadai da yunƙurin kisan tsohon shugaban Amurka, Donald Trump.

Trump wanda ke yin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Republican, ya tsallake rijiya da baya bayan an harbe shi, yana cikin jawabi a wajen yaƙin neman zaɓe, a Pennsylvania, lamarin da shugaban Najeriyan ya bayyana a matsayin babban tashin hankali.

Tinubu ya bi sahun sauran shugabannin duniya wajen bayyana takaici a kan harin, yana mai cewa irin wannan rikici bashi da mazauni a turbar dimokuraɗiyya.

A saƙon da Tinubu ya wallafa a shafin X yace harin da aka kai wa tsohon shugaban Amurka, Donald Trump babban abin tashin hankali ne kuma ya saɓawa turbar dimokuraɗiyya.

Sannan kuma ya miƙa jajen sa ga tsohon shugaban ƙasar, tare yi masa fatan samun sauki cikin sauri, gami da da mika ta’aziya ga ƴan uwan wanda ya mutu a harin.

Daga bisani Tinubu ya ce Najeriya tana tare da Amurka a wannan yanayi na alhini.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp