Home DUNIYA Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin saman Nijeriya tace ta sami nasarar tarwatsa maboya ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, a garin kufam shantu dake karamar hukumar giwa dake jihar kaduna a arewa maso yammacin kasar Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na rundunar Air vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar a ranar lahadi.

Sanarwar ta ce daya daga cikin atisayen da rundunar sojin ta kai a ranar 12 ga watan Yuni a maboyar ‘yan ta’adda ta Alhaji layi, wadda suka sami nasarar tarwatsa ta da kuma kometa.

Haka kuma a wani harin makamancin wannan da rundunar ta gudanar ranar 13 ga watan na Yuni kan ‘yan bindigar a cikin dajin malum dake karamar hukumar Igabi, wadda rundunar ta ce ta sami gagarumar nasara.

Jihar kaduna dai na guda cikin jihohin dake arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro da suka addabi al’ummar ta musamman masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp