Home DUNIYA Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ta tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar Sojojin saman Nijeriya tace ta sami nasarar tarwatsa maboya ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, a garin kufam shantu dake karamar hukumar giwa dake jihar kaduna a arewa maso yammacin kasar Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na rundunar Air vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar a ranar lahadi.

Sanarwar ta ce daya daga cikin atisayen da rundunar sojin ta kai a ranar 12 ga watan Yuni a maboyar ‘yan ta’adda ta Alhaji layi, wadda suka sami nasarar tarwatsa ta da kuma kometa.

Haka kuma a wani harin makamancin wannan da rundunar ta gudanar ranar 13 ga watan na Yuni kan ‘yan bindigar a cikin dajin malum dake karamar hukumar Igabi, wadda rundunar ta ce ta sami gagarumar nasara.

Jihar kaduna dai na guda cikin jihohin dake arewacin Nijeriya dake fama da matsalolin rashin tsaro da suka addabi al’ummar ta musamman masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp