Home DUNIYA Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba...

Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba – Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bazai saci dukiyar Al’ummar jihar kano ba, kuma bazai bari a satar musu kudi ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yammacin asabar yayin da yake kaddamar da kasha na biyu na rabon tallafi ga Al’ummar kananan hukumomi 44 dake fadin jihar nan.

Abba ya bayyana cewa gwamnatinsa baza ta saci kudin al’ummar jihar ba, sannan kuma zata dauki matakin hukunta dukkan wanda ya saci kudin a karkashin kulawarsa.

Gwamnan yace zasu raba miliyan 260 ga mata 5,200 wadanda suka fito daga kananan hukumomin jihar 44, wanda kowacce zata sami naira dubu 50, wanda zai taimakesu wajen sanya jari.

Haka kuma yace zasu cigaba da taimakawa matan dake kananan hukumomin da naira miliyan 260 a dukkanin wata har zuwa karshen wa’adin mulkin sa.

Yace wannan na cikin kudirin su da kuma abinda suka yi al’ummar jihar alkawari a yayin yakin neman zabe, kuma wannan na matsayin sakayya da zasu yiwa mata bisa gudunmawar da suka bayar wajen kafa gwamnatin.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp