Home DUNIYA Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba...

Ba zamu saci kudin ku ba, ba zamu bari a sata ba – Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bazai saci dukiyar Al’ummar jihar kano ba, kuma bazai bari a satar musu kudi ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yammacin asabar yayin da yake kaddamar da kasha na biyu na rabon tallafi ga Al’ummar kananan hukumomi 44 dake fadin jihar nan.

Abba ya bayyana cewa gwamnatinsa baza ta saci kudin al’ummar jihar ba, sannan kuma zata dauki matakin hukunta dukkan wanda ya saci kudin a karkashin kulawarsa.

Gwamnan yace zasu raba miliyan 260 ga mata 5,200 wadanda suka fito daga kananan hukumomin jihar 44, wanda kowacce zata sami naira dubu 50, wanda zai taimakesu wajen sanya jari.

Haka kuma yace zasu cigaba da taimakawa matan dake kananan hukumomin da naira miliyan 260 a dukkanin wata har zuwa karshen wa’adin mulkin sa.

Yace wannan na cikin kudirin su da kuma abinda suka yi al’ummar jihar alkawari a yayin yakin neman zabe, kuma wannan na matsayin sakayya da zasu yiwa mata bisa gudunmawar da suka bayar wajen kafa gwamnatin.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp