Home DUNIYA An ceto mutum 4 cikin wadanda gini ya rufta kan su a...

An ceto mutum 4 cikin wadanda gini ya rufta kan su a Abuja

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na tabbatar da cewa wani gini mai hawa biyu ya rushe, tuni dai hukumomin ceto suka ce sun kuɓutar da mutum huɗu da ke karkashin bara guzai ginin

Lamarin ya auku ne a unguwar kubwa phase 2 da misalin karfe 7 na safiyar asabar.

Masu aikin ceto da jami’an tsaro na ci gaba da neman mutanen da ginin ya rufta da su.

Gidan ya rushe ne kwana ɗaya bayan wata makaranta ta rushe a jihar Filato, inda ya kashemutum 22 ya kuma raunata wasu 132.

Kwanaki 11 da suka wuce ma wani ginin ya rushe a unguwar Area 11 da ke yankin Garki a birnin Abuja.

An ruwaito cewa gidan tun da fari Otal ne mai suna Al-hilal, sai dai daga bisani aka mayar dashi gidan kwana.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp