• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home DUNIYA SWAN ta yi Allah wadai da yanayin da Kano Pillars ke ciki
  • DUNIYA
  • General
  • Labarai

SWAN ta yi Allah wadai da yanayin da Kano Pillars ke ciki

By
Ibrahim Ibrahim Nafiu
-
July 15, 2024
Arewa Award

Kungiyar marubuta labarin wasanni ta kasa reshen jihar Kano (SWAN) ta ja hankalin gwamnatin jihar da ta sanya kwararrun mutane dake da ilimi a fannin wasanni wajen jagorantar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars dama sauran harkokin wasanni, domin inganta harkokin wasanni a jihar.

Wannan na cikin wani sanarwa da kungiyar ta fitar ta bakin shugaban kungiyar na jiha wanda sakataren ta Zaharaddini Sale da Muhammad Nura Tijjani suka sanya wa hannu.

Kungiyar tayi kira da gwamnati ta gaggauta gyara da kuma daga likafar filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata yayin da ta bukaci gyara da kwaskware filin wasa na Mahaha duka domin inganta harkokin wasannni a jihar.

Kungiyar tace dole a kalli filin wasan gargajiya na Ado Bayero Square domin bashi fifiko kasancewar yanzu duniya ta juya kan inganta wasannin gargajiya domin farfado da al’adun al’umma.

Read Also:

  • DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya
  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

a yunkurinta na inganta harkokin wasanni a jihar kano SWAN ta fitar da jadawalin kwamitin kwararru da masu bada shawara bisa cikakken tsari domin tabbatar da cigaban harkokin harkokin wasanni a jihar musamman abin da ya shafi kungiyar Kano pillars.

kazalika kungiyar ta yi Allah wadai da yanayin da kano pillars ta tsinci kanta a ciki,”mun fahimci halin da kungiyar ke ciki kuma muna tare da su wajen warware matsalolin kama daga kan yan wasa, shuwagabanni da kuma masu horarwa.

“Don haka muna kira da gwamnati ta hada kai da duk masu ruwa da tsaki domin kawo karshen matsalolin da kuma inganta harkokin wasanni a jihar.

idan za’a tuna kungiyar ta Pillars ta fuskanci matsaloli a baya bayannan wanda hakan ya haddasa rabuwar kan jagororin kungiyar gida biyu.

sa idai zuwan sabon kwamishinan wasanni a jihar Mustapha Rabi’u Kwankwaso yayi yunkurin kawo sauyi wanda ya sa aka samu sabon mai horarwa a kungiyar.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 20 hours 31 minutes 20 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 12 minutes 46 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleKu daina bayyana kan ku matsayin sarakai – Umarnin Kotu ga Tsofaffin Sarakunan Kano
Next articleUAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya
Ibrahim Ibrahim Nafiu

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya

Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Bom ya kashe masu yawon murnar sallah a Sakkwato

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a Zamfara

An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

Gwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Jirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga’

Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 ‘yan asalin Kano

Recent Posts

  • DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya
  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu
  • Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 20 hours 31 minutes 21 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 12 minutes 46 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiyaNajeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu - OPECTinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyyaA aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a ManguNajeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga SaudiyaBom ya kashe masu yawon murnar sallah a SakkwatoNan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya - DangoteSojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a ZamfaraAn samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari MansurGwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man feturJirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga'Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 'yan asalin KanoGwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci - NLCSojoji sun ce sun hallaka ƴan ta'adda 60 a jihar BornoAn kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a Kano
X whatsapp